Matawalle ya nemi taimakon Bazoum kan matsalar ƴan bindiga a Zamfara

Wannan shafi ne da ke kawo maku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran kasashen duniya.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail

  1. Yarjejeniyar Iran da ƙasashen Yamma na barazanar rugujewa

    Iran

    Asalin hoton, AFP

    Jami'an diflomasiyya daga Birtaniya da Faransa da Jamus sun yi gargadin cewa yarjejeniyar nukiliya ta 2015 na cikin hatsarin "rugujewa idan aka yi la'akari da yadda Iran ke hanzarta shirinta na nukiliya".

    Sun ce suna bai wa Iran ɗin lokaci a tattaunawar da suke yi a Vienna saboda tana aiwatar da wasu abubuwa da suka saba wa yarjejeniyar.

    Wakiliyar BBC ta ce a ganinsu Iran na jan kafa ne a tattunawar da suke yi domin ta kara inganta shirin nukliyarta.

    Sai dai jakadan Iran a Biritaniya, Mohsen Baharvand, ya shaida wa BBC cewa har yanzu Iran din na da aniyar aiwatar da ka'idojin yarjejeniyar da ta cimma da kasashen Yamma.

  2. Korona ta sake kashe mutum biyu a Najeriya, 385 sun kamu

    Korona

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar daƙile cutuka masu yaɗuwa a Najeriya, NCDC, ta ce karin mutum 385 ne suka kamu da cutar korona a faɗin ƙasar ranar Litinin, 13 ga watan Disamba 2021.

    Kazalika, cutar ta kashe ƙarin mutum biyu, abin da ya sa jumillarsu ta zama 2,983.

    Daga cikin sabbin wadanda suka kamu, babban birnin Nijeriya Abuja ne kan gaba da mutum 116, sai jihar Delta mai 115, da jihar Akwa Ibom 41, sai Ogun mai 33.

    Jihar Cross Rivers da Edo na da mutum 23 kowaccensu yayin da Kaduna take da 10. Jihar Rivers kuwa na da 7, Bayelsa da Oyo na da 5 kowaccensu yayin da Kano ke da 2.

    Yanzu dai adadin waɗanda suka kamu da cutar a Najeriya ya kai 217,866 amma kuma an sallami 210,706 daga asibiti.

  3. 'Yan fashin daji sun sace mutane a kan titin Kaduna zuwa Zariya

    'Yan fashin daji

    Asalin hoton, Daily Trust

    Rahotanni na cewa an kashe mutane da dama tare da sace wasu yayin da 'yan fashi suka buɗe wa matafiya wuta a kan babbar hanyar Kaduna zuwa Zariya ranar Litinin da dare.

    Jaridar Daily Nigerian ta ruwaito cewa maharan sun fara harbe-harben ne a daidai garin Kofar Gayan da ke kusa da birnin Zariya da misalin ƙarfe 8:00.

    Wasu da suka shaida lamarin sun bayyana wa jaridar cewa 'yan bindigar sun buɗe wuta kan mai tsautsayi ne don su tashi hankalin matafiyan da zimmar yin garkuwa da su.

    Hakan ta sa suka yi awon gaba da wasu zuwa cikin daji kafin isowar jami'an tsaro, a cewar shaidun.

    'Yan Najeriya da na ci gaba da zanga-zanga tare da sukar gwamnatin Shugaba Buhari, suna masu zargin ta da gazawa wajen daƙile matsalar tsaro a yankin arewa maso yamma, inda shugaban ya fito.

    A makon da ya gabata wasu 'yan bindiga suka ƙona matafiya 23 a cikin motar bas a Jihar Sokoto, abin da ya jawo ɓacin rai da zanga-zanga a shafukan zumunta.

    Gwamnatin ta Buhari na cewa tana bakin ƙoƙarinta don shawo kan matsalar, inda ta tura shugabannin tsaron ƙasar zuwa ziyarar gani-da-ido a jihohin Sokoto da Katsina.

  4. Barka da shigowa

    Mun sake haɗuwa da ku a shafin labarai kai-tsaye, wanda zai kawo rahotanni kan abubuwan da ke faruwa a sassan duniya.

    Hankalinmu zai fi karkata a Najeriya da Nijar da maƙotansu.

    Umar Mikail ne ke tare da ku a wannan hantsi.