Gwamnatin Kaduna za ta kori malaman makaranta 233

Wannan shafi ne da ke kawo maku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran kasashen duniya.

Rahoto kai-tsaye

Mustapha Musa Kaita

  1. Ana shirin ɗaukar ƴan banga don gadin makarantun Abuja

    Yan banga

    Asalin hoton, Other

    Hukumomin birnin Tarayya Abuja na Najeriya sun ce suna shirin ɗaukar ƴan banga domin gadin makarantu saboda barazanar tsaro da ake fuskanta.

    Jaridar The Punch ta ambato daraktan gudanarwa a ɓangaren tsaro na hukumar birnin na tarayya yana cewa an riga an kammala shirin ɗaukar ƴan banga da za su tabbatar da tsaron makarantu a faɗin yankin na Abuja.

    Wannan zuwa ne biyo bayan wasu rahotanni na tsaro da ke cewa ƴan bindiga daga jihohin da ke makwabtaka da Abuja na tsallakowa zuwa birnin na tarayya.

    Ƴan bindiga sun sha kai hare-hare makarantu suna satar ɗalibai a yankin arewa maso gabashi, kuma ana ganin satar mutane ta dawo a hanyar Kaduna zuwa Abuja.

    A makon da ya gabata gwamnatin Neja da ke makwabtaka da Abuja ta yi gargaɗin cewa mayaƙan Boko Haram sun mamaye wasu yankuna na jihar.

  2. Korona ta kama mutum 4 a Kaduna

    Hukumar daƙile cutuka masu yaɗuwa a Najeriya, NCDC, ta ce karin mutum 52 ne suka kamu da cutar korona a faɗin ƙasar ranar Laraba.

    Daga cikin sabbin wadanda suka kamu, Lagos na da mutum 29 sai Abuja da ke da mutum 21.

    A jihar Kaduna an samu ƙarin mutum huɗu.

    JIhar Bauchi na da mutum uku sai Kanoda ke da mutum biyu.

    Ita kuwa Filato na da mutum biyar.

    A jihar Ogun da Oyo an samu mutum mutum ɗaya kowanensu.

    Yanzu jimullar waɗanda suka kamu da cutar a Najeriya tun bayan ɓullarta sun kai 214,270 ko da yake an sallami 207,312.

    Adadin waɗanda suka rasa rayukansu sanadin cutar kuwa ya kai 2,978.

  3. Maraba

    Muna maku maraba da kasancewa da mu a wannan shafin da za mu kawo maku labarai da rahotanni kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya.