Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Kunamu sun harbi mutum 450 a Masar, uku sun mutu

Wannan shafi ne da ke kawo maku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran kasashen duniya.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail and Mustapha Musa Kaita

  1. Sai gobe...

      • Marubuci, Mustapha Musa Kaita
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, Multi-Media Broadcast Journalist

    Masu bibiyarmu a wannan shafin a nan muka zo ƙarshen kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye, sai kuma gobe Lahadi idan Allah ya kai mu za mu ci gaba da kawo muku wasu labaran.

    Za ku iya ziyartar shafinmu na Facebook ko Twitter ko kuma na Instagram domin samun ƙarin bayani kan wasu labaran da muka wallafa ko kuma tafka muhawara a kansu.

    Ga wasu daga cikin labaran da muka wallafa a wannan shafin:

    • Ƙwazon 'yan Najeriya a ƙasashen waje saboda ilimin da suka samu a gida ne - Buhari
    • Kotu ta ɗaure ɗan majalisa a Tunisia saboda cin zarafin ɗaliba
    • Mutum 10 sun ƙone ƙurmus a hatsarin mota a Jihar Ondo
    • Buhari ya wuce Afirka ta Kudu daga Faransa
    • Gwamna Matawalle ya gabatar da buƙatun Zamfara a taron sauyin yanayi
    • Ana daf da sanar da Dean Smith a matsayin sabon kocin Norwich City
    • Dakarun Sudan sun harba hayaƙi mai sa hawaye domin tarwatsa masu zanga-zanga
    • Poland na zargin Belarus da rura wutar kan iyaka

    Za ku iya duba ƙasa domin karanta waɗannan labran da ma wasu muhimmai

  2. An kashe masu zanga-zanga biyar a Sudan

    Rahotanni daga Sudan na cewa an kashe mutum biyar daga cikin masu zanga-zangar goyon bayan dimokraɗiyya a Sudan, kamar yadda ƙungiyar likitocin ƙasar ta tabbatar.

    Ƙungiyar ta tabbatar da cewa huɗu daga cikin masu zanga-zangar sun rasu ne sakamakon harbin bindiga, mutum daya kuma ya rasu ne bayan ya ƙware sakamakon hayaƙi mai sa hawaye da ya shaƙa.

    Ƴan sanda a ƙasar dai sun musanta amfani da harsasai, inda suka ce sun yi amfani da ƙarfi kaɗan.

    Gidan talabijin na ƙasar ya ruwaito cewa ƴan sanda 39 na ƙasar sun ji mummunan rauni yayin arangama da masu zanga-zangar.

    Mummunar arangamar na zuwa ne kwanaki bayan sojoji sun sake wani juyin mulki a ƙasar.

  3. Harin bam ya halaka wani ɗan jarida a Afghanistan

    Wani ɗan jaridar Afghanistan, Hamid Saighani ya rasu a lokacin da bam ya tashi da shi a wani hari da aka kai wa wata babbar mota a Kabul babban birnin ƙasar.

    Ɗan jaridar tsohon gabatar da shirye-shirye ne a gidan talabijin ɗin Ariana da ke ƙasar.

    Wani jami'in Taliban ya bayyana cewa akwai wasu mutum biyu da suka samu rauni a lokacin da lamarin ya faru.

    Jami'ai a yankin da lamarin ya faru sun bayar da adadi mai yawa na mutanen da suka jikkata. Babu wata ƙungiya da ta ɗauki nauyin kai wannan harin amma mayaƙan IS da ke iƙirarin jihadi sun kai hare-haren bam irin haka a yankin a baya.

  4. An kashe fursnoni 58 yayin arangama a Ecuador

    Hukumomi a Ecuador sun bayana cewa aƙalla mutum 58 aka kashe yayin wata arangama tsakanin gungun fursunoni masu adawa da juna a gidan yarin Guayaquil.

    Sun ƙara da cewa an kiyaye kisan wasu ƙarin fursunonin bayan da ƴan sanda suka kutsa gidan yarin domin kwantar da tarzomar.

    Aƙalla mutum 10 ne suka samu raunuka a yayin tarzomar da ta ɓarke a gidan yarin.

    A dai wannan gidan yarin ne aka taɓa yin wata mummunar tarzoma a watan Satumba inda aka kashe mutum 119.

    Dama gidajen yarin Ecuador akasari a cike suke da mutane kuma ana yawan samun munanan rikice-rikice tsakanin gungu-gungu masu adawa da juna.

  5. Kunamu sun harbi mutum 450 a Masar, uku sun mutu

    Rahotanni daga Masar na cewa kunamu sun kashe mutum uku a kudancin birnin Aswan bayan ruwan sama mai ƙarfi ya jawo su kan tituna da cikin gidajen mutane.

    Ma'aikatar lafiya ta ƙasar ta tabbatar da cewa aƙalla mutum 450 ne kunama ta harba.

    Ruwan da aka yi a kusa da Kogin Nilu a ranar Juma'a na da ƙarfi ƙwarai kamar yadda rahotanni suka tabbatar.

    Dama ruwan sama mai ƙarfi ya saba sharo kunamu kan tituna, a wani lokacin ma har da macizai.

    Tuni gwamnatin ƙasar ta aika da magungunan kashe dafin kunama da macizai zuwa asibitoci da ke ƙauyukan da ke gefen tsaunuka da sahara.

  6. Gurɓatacciyar iska ta sa ma'aikata da dalibai zaman gida na kwana huɗu a Delhi

    Hukumomi a Delhi babban birnin Indiya sun buƙaci ma'aikatan gwamnati da su yi aiki daga gida haka zalika makarantu su koma karatu ta intanet na tsawon mako guda sakamakon ƙaruwar gurɓatacciyar iska.

    Babban ministan ƙasar, Arvind Kejriwal wanda ya sanar da hakan ya kuma ce a dakatar da ayyukan gine-gine har na kwanaki huɗu daga gobe Lahadi.

    Wannan matakin na zuwa ne bayan da Kotun Ƙolin Indiya ta buƙaci gwamnatin ƙasar ta fito da matakan gaggawa domin daƙile bazuwar gurɓatacciyar iska a birnin na Delhi.

    Delhi na fuskantar gurɓacewar iska musamman a lokacin hunturu sakamakon ƙona gonaki bayan girbi da kuma hayaƙin da ke fitowa daga motoci da sauran abubuwan sufuri.

    Delhi ne birnin da aka yi itifaƙi a duniya ya fi kowane birni gurɓatacciyar iska.

  7. Togo ta tabbatar da harin masu iƙirarin jihadi kan jami'anta

    Gwamnatin ƙasar Togo ta tabbatar da cewa wasu da ake zargin masu iƙirarin jihadi ne sun kai hari a arewacin ƙasar kwanaki kaɗan da suka gabata.

    Maharan waɗanda ke ɗauke da makamai sun kai harin ne a wani wurin da jami'an tsaron ƙasar suke a kusa da iyakar ƙasar da Burkina Faso, yankin da hare-haren masu iƙirarin jihadi ke ƙara ƙamari.

    Shugaban ƙasar Togo, Faure Gnassingbe ya ziyarci wurin da lamarin ya faru inda ya buƙaci sojojin ƙasar da farar hula su yi aiki tare domin kawo ƙarshen ƴan tayar da ƙayar bayan.

    A baya dai ƙasar ta Togo ba ta cika fama da rikice-rikicen masu iƙirarin jihadi ba sai dai ƴan bindigan na ta bazuwa zuwa kudancin ƙasar daga yankin Sahel da suka fi ƙarfi.

  8. Sarkin Kuwait ya yi wa fursunoni 35 afuwa

    Sarkin Kuwait ya yi wata doka inda ya yafe wa wasu mutum 35 zaman gidan yari.

    Har yanzu dai ba a sanar da sunayen mutanen da Sheikh Nawaf al-Ahmad al-Sabah ya yi wa wannan rangwamen ba.

    A gobe Lahadi ne ake sa ran gidan jaridar ƙasar zai wallafa sunayen.

    Tuni dama ƴan adawa daga majalisar dokokin ƙasar suka yi ta neman a yi wa ƴan adawar da ke tsare afuwa wanda hakan zai zama wata hanya ta kawo ƙarshe rashin jituwar da aka daɗe ana samu tsakaninsu da gwamnatin ƙasar.

    Zaman doya da manja tsakanin ƴan adawa a Kuwait da kuma gwamnatin ƙasar ya jawo tafiyar hawainiya matuƙa musamman a wajen aiwatar da tsare-tsare da ayyukan ƙasar.

  9. An kama ɗan sandan da ake zargi da kashe yarinya a Kamaru

    Hukumomi sun kama ɗan sandan da ake zargi da harbe wata yarinya mai shekara takwas a Kamaru.

    Ɗan sandan ya yi harbi kan wata mota da ta tsere wa wurin duba ababen hawa ranar Juma'a a birnin Bamenda da ke fama da tashin hankali na 'yan tawaye.

    Mutuwar yarinyar ta jawo zanga-zanga a yammacin Juma'a inda aka raunata aƙalla mutum biyu. Kafafen yaɗa labarai na ƙasar sun ruwaito cewa jami'an tsaro sun buɗe wa 'yan zanga-zangar wuta.

    Sai dai wani soja da ke wurin ya ce jami'an tsaron sun yi harbi a sama ne don tarwatsa mutanen.

    Bamenda ne babban birnin ɗaya daga cikin biyu na yankunan rainon Ingila da ke fama da fafutikar tawaye, inda mayaƙan ke iƙirarin cewa gwamnatin ƙasar na zalintarsu.

  10. Poland na zargin Belarus da rura wutar kan iyaka

    Shugaban tsaron ƙasar Poland na zargin Belarus da ƙara rura wutar rikicin da ke faruwa kan iyakar ƙasashen ta hanyar lalata wani sashe na katanga domin bai wa ƴan ci rani damar kwarara.

    Stanislaw Zaryn ya ce lamarin wanda ya faru cikin dare guda kusa da garin Czeremcha a matsayin wani abu da aka shirya.

    Poland ta ce dakarun Belarus sun yi amfani da mota domin lalata katangar, inda suka kashe wa jami'an da ke gadin iyakar ido da fitila mai haske da kuma bai wa ƴan ci rani hayaƙi mai sa hawaye.

    A wani ɓangaren kan iyakar kuma, wakilin BBC ya tabbatar da cewa dubban ƴan ci rani waɗanda akasarinsu Ƙurdawa ne daga Iraƙi sun yada zango a Belarus a cikin irin tantunan da ake yi a sansanoni wadanda ba za su iya basu kariya daga sanyin da ke tafe ba.

  11. Dakarun Sudan sun harba hayaƙi mai sa hawaye domin tarwatsa masu zanga-zanga

    Jami'an tsaron Sudan sun harba hayaƙi mai sa hawaye domin tarwatsa masu zanga-zanga a Khartoum a yau Asabar, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito.

    Masu zanga-zangar sun taru ne domin nuna rashin goyon bayansu kan ƙwace mulkin ƙasar da sojin ƙasar suka sake yi a makon da ya gabata.

    Hakazalika wannan zanga-zangar na zuwa ne kwanaki biyu bayan da shugaban mulkin soja a ƙasar Abdel Fattah al-Burhan ya sanar da kafa sabuwar majalisar mulkin ƙasar wadda a ciki babu gamayyar farar hula wadda aka rinƙa mulkin ƙasar da ita tun a 2019.

    Masu goyon bayan dimokraɗiyya a ƙasar sun yi Allah wadai da wannan yunƙurin tare da lasar takobin ci gaba da saɓa wa gwamnatin sojin ƙasar ta hanyar gudanar da zanga-zanga kan juyin mulkin da aka yi a ranar 25 ga watan Oktoba.

    A yau Asabar, jami'an tsaro sun rufe gadoji da ke tsakanin tsakiyar Khartoum da birnin Omdurman da Arewacin Khartoum inda aka hana motoci da masu tafiya a ƙafa wucewa ta hanyar saka shingen waya mai ƙayoyi.

  12. 'Yan bindiga sun kashe sojojin Kamaru biyar

    Sojojin Kamaru aƙalla biyar ne aka kashe a wani hari da 'yan bindiga suka kai Matazem da ke kusa da Bamenda na arewa maso yammacin ƙasar.

    Rahotanni sun ce mayaƙan 'yan tawaye ne suka yi musu kwanton-ɓauna inda abin hawansu ya taka abin fashewa, abin da ya sa wasu suka ji rauni.

    Wata majiya ta faɗa wa kafar labarai ta MMI cewa an rufe hanyar.

    "Ba za mu iya gudanar da komai ba, harbe-harbe ake yi ta ko'ina," a cewar majiyar.

  13. Ana daf da sanar da Dean Smith a matsayin sabon kocin Norwich City

    Dean Smith na daf da zama sabon kocin Norwich City

    A halin yanzu ana kammala shirye-shiryen da ake da su a ƙasa domin tsohon kocin na Aston Villa ya maye gurbin Daniel Farke wanda Norwich City ɗin ta kora a makon da ya gabata.

    Ana sa ran Craig Shakespeare, wanda ya yi aiki tare da Smith a Villa ya zama mataimakinsa kuma gobe Lahadi ko kuma jibi Litinin ake ganin za a fitar da sanarwa.

    Tuni tsohon kocin Chelsea Frank Lampard ya janye aniyarsa ta neman kujerar kocin na Norwich City.

    A ranar 20 ga watan Nuwamba ne kulob ɗin zai buga wasansa na gaba na gasar Premier da Southampton.

  14. Gwamna Matawalle ya gabatar da buƙatun Zamfara a taron sauyin yanayi

    A ranar Juma'a ne aka kawo karshen taron Majalisar Dinkin Duniya (MDD) kan sauyin yanayi a birnin Glasgow na Birtaniya.

    Gwamnatoci da kwararru ne suka hadu domin samun mafita game da yadda duniya ke kara dumama da nufin samo hanyoyin warware matsalolin.

    Gwamnan Jihar Zamfara a Najeriya, Bello Muhammad Matawalle, shi ma ya halarci wannan taro, inda ya gabatar da bukatun jiharsa.

    A cikin wata hira da Ahmad Abba Abdullahi, ya fara ne da yi masa bayani kan abubuwan da ya gabatar a wajen taron, kafin su tattauna kan kalubalen tsaron da jiharsa ke fuskanta.

  15. Mayaƙan ISWAP sun kai wa sojoji hari a garin Askira na Jihar Borno

    Wasu mahara da ake kyautata zaton mayaƙan ƙungiyar Islamic State of West Africa Province(ISWAP) ne sun kai wa sansanin sojoji na Ƙaramar Hukumar Askira/Uba ta Jihar Borno, a cewar rahoton Daily Trust.

    Wasu mazauna garin sun faɗa wa jaridar cewa sun hangi mayaƙan a kan hanyarsu a cikin manyan motoci masu ɗauke da bindigogi da safiyar Asabar kuma suka kai rahoto ga jami'an tsaro kafin su kai harin.

    Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Borno, Abdullahi Musa Askira, ya ce an tabbatar masa da faruwar lamarin.

    Wani ɗan banga mai suna Yakubu Luka, ya ce mayaƙan sun wuce kai-tsaye zuwa barikin sojojin bayan sun shiga garin.

    "E, yanzu haka ISWAP na kai wa garin Askira hari amma an faɗa mani cewa jami'an tsaronmu na fafatawa da su. Mazauna garin na cikin daji," in ji ɗan majalisar.

    "Mutanena sun faɗa mani cewa 'yan bindigar sun je da motoci masu bindiga, mutane sun firgita a faɗin garin."

  16. An kwashe mutanen da suka maƙale a wurin shaƙatawa a Amurka

    A wani abu da ake alakantawa da dumamar yanayin, jami'ai a jihar Oregon da ke yammacin Amurka sun ce jirage masu saukar ungulu sun kwashe mutum 20 da suka makale a wani wurin shakatawa na matafiya.

    Wani kogi da ya tumbatsa saboda tsananin ruwan sama ne ya malala a wuraren da ke kusa da Neskowin, kudu maso yammacin Portland.

    Ana umartar mutanen da ke zaune a yankin su kasance cikin shirin ko-ta-kwana saboda ambaliyar na kan hanyar dosar su.

    Irin wadannan bala'o'i na daga cikin abubuwan da ake dangantawa da tasirin sauyin yanayi, wanda mahalarta taron Glasgow ke ganin cewa ya kamata a shawo kansu.

  17. Buhari ya wuce Afirka ta Kudu daga Faransa

    Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bar birnin Paris na Faransa a yau Asabar zuwa Afirka ta Kudu domin halartar taron kasuwanci na ƙasashen Afirka.

    Femi Adesina, mai magana da yawun fadar shugban ƙasa, ya ce za a gudanar da taron ne daga 15 zuwa 21 ga watan Nuwamba, wanda bankin kasuwanci na Afirka, AFREXIM, ke shiryawa da haɗin gwiwar hukumar ƙasashen Afirka ta AUC.

    "A ranar Asabar Shugaba Buhari zai bar Paris zuwa Durban na Afirka ta Kudu bisa gayyatar da Shugaba Cyril Ramaphosa ya yi masa don haɗuwa da sauran shugabannin Afirka a wurin taron Baje-Kolin Afirka 2021," a cewarsa.

    Ya ce za fara taron ne ranar Litinin.

    Buhari ya bar Najeriya ranar 31 ga watan Oktoba kwana biyu bayan ya koma gida daga Saudiyya, inda ya halarci taron sauyin yanayi a Birtaniya kafin daga baya ya wuce Faransa wurin taron zaman lafiya tare da Shugaban Faransa Emanuel macron.

    Ana sa ran zai koma Najeriya ranar Talata 16 ga watan Nuwamba.

  18. Mutum 10 sun ƙone ƙurmus a hatsarin mota a Jihar Ondo

    Mutane da dama ne suka rasu ranar Juma'a sakamakon wani mummunan hatsarin mota da ya faru a Jihar Ondo da ke kudancin Najeriya.

    Shaidu sun ce mutanen sun ƙone ƙurmus ta yadda ba a iya gane su sannan wasu biyar sun ji munanan rauni.

    Kamfanin dillancin labarai na NAN ya ruwaito cewa hatsarin ya faru ne sakamakon karo da wata bas ƙirar Toyota Coasta ta yi da wata Ford J5, inda nan take suka kama da wuta.

    Wani wanda lamarin ya faru kan idonsa ya faɗa wa NAN cewa fasinjojin bas ɗin sun dawo daga wani taro ne zuwa Akure, babban birnin jihar.

    Ya ce aƙalla mutum 10 ne suka mutu a hatsarin, yayin da J5 ɗin mai ɗauke da barasa da kuma bas suka yi yunƙurin kauce wa wani rami da ke kan titin Ore-Okitipupa.

  19. Barcelona ta sake ɗaukar Dani Alves

    Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barcelona ta cimma yarjejeniya da tsohon ɗan wasanta Dani Alves domin sake ɗaukarsa bayan shekara biyar da barinsa ƙungiyar.

    Alves mai shekara 38 wanda ya lashe manyan gasa tara a Barca da Juventus da Paris St-Germain, zai koma kulob ɗin na Spain a kyauta don kammala wasannin gasar 2021-22.

    Ɗan ƙasar Brazil ɗin ya shafe shekara takwas a Barca daga 2008 zuwa 2016, inda ya lashe La Liga shida da Zakarun Turai uku da kuma Copa del Rey huɗu.

    Ƙungiyar ta siffanta shi da "ɗan wasan baya na gefen dama mafi ƙwarewa a tarihin Barca" cikin wata sanarwa a shafinta.

    "Ɗan wasan zai isa Barca a mako mai zuwa amma ba zai iya buga wasa ba har sai watan Janairu," in ji sanarwar.

    Tun farko Barca ta fasa ɗaukar Alves amma sabon mai horarwa Xavi ya nuna sha'awar dawo da shi tawagar domin taimaka mata dawowa kan ganiya.

    A watan Satumba aka dakatar da kwantiraginsa a ƙungiyar Sao Paulo sakamakon rikici kan albashinsa.

  20. Kotu ta ɗaure ɗan majalisa a Tunisia saboda cin zarafin ɗaliba

    Kotu ta ɗaure wani ɗan majalisa a Tunisia ranar Juma'a sakamakon kama shi da laifin cin zarafin wata ɗaliba ta hanyar rashin ɗa'a, a cewar lauyan ɗalibar.

    Zouhair Makhlouf ɗan majalisa ne maras jam'iyya kuma zai yi zaman shekara ɗaya a gidan yari.

    A watan Oktoban 2019 ne aka ga ɗan majalisar yana aikata lalata a cikin motarsa a birnin Nabeul.

    Ɗalibar da ta ɗauki hotunansa - wadda ba ta kai shekara 18 ba a lokacin - ta wallafa su a shafukan zumunta kuma ta ce ya bi ta har makaranta yana mai zarginta da tsangwamarsa.

    Yayin zaman kotun ya faɗa cewa yana ɗauke da cutar siga ne kuma a lokacin yana ƙoƙari ne ya yi fitsari a cikin wata kwalaba cikin gaggawa.

    Lauyan ɗalibar ta ce kotu ta same shi da laifin cin zarafi ta hanyar nuna rashin ɗa'a.