Ƴan sanda sun kama wasu masu zanga-zangar tunawa da Endsars a Legas

Ƴan sanda a Legas sun kama a ƙalla mutum shidda da suka fita zanga-zangar tunawa da kashe-kashen Lekki.
Wannan na zuwa ne a lokacin da ƴan sandan suka taru bayan sun yi gargaɗin cewa kada wanda ya fito zanga-zanga a yau amma ana iya yin jerin gwanon motoci.
Mai barkwanci nan na Najeriya Mista Macaroni da mawaƙi Falz ranar Litinin sun sanar da cewa za a yi zanga-zangar duk da gargaɗin na ƴan sanda.
Zanga-zangar wadda ake gudanarwa yau Laraba don tunawa ce da abin da ya faru a zanga-zangar Endsars ta bara.
Zanga-zangar dai ta nuna ƙin jinin abin da aka kira cin zarafin da ƴan sanda ke yi ce, amma daga baya ƴan banga suka shiga zanga-zangar kuma nan da nan lamurra suka rikice.
Ɗaya daga cikin abubuwan da suka faru kuma ya zama babban lamari ranar 20 ga watan Oktoba 2020, shi ne harbe-harben da aka yi a dandalin Lekki toll gate.
An yi zargin cewa jim kaɗan bayan faɗuwar rana, sojoji sun je dandalin na Lekki don tarwatsa masu zanga-zangar saboda dokar hana fita da gwamnan jihar ya sa.
Wasu mutane sun yi ta yaɗa hotunan a shafukan sada zumunta inda suka yi ikirarin cewa sojoji sun kashe mutane da dama a ranar.
Rundunar sojin Najeriya ta amice ta yi harbi a Lekki a ranar a lokacin zanga-znagar amma sun ce ba su harba harsasai ba kuma ba su kashe kowa ba.



