Sojoji sun dakile hari kan tubabbun 'yan Boko Haram

Wannan shafi ne da ke kawo maku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran kasashen duniya

Rahoto kai-tsaye

Awwal Ahmad Janyau

  1. Ƙarin mutum 32 sun kamu da korona a Kaduna

    Hukumar daƙile cutuka masu yaɗuwa ta Najeriya ta ce ƙarin mutum 161 sun kamu da

    korona a ranar Juma’a a ƙasar.

    Alƙalumman sun nuna cewa an samu ƙarin mutum 45 da suka kamu da cutar a Lagos, yayin da kuma ƙarin mutum 32 suka kamu a Kaduna.

    A jihar Zamfara mai fama da matsalar tsaro an samu mutum biyar da suka kamu da cutar a ranar Juma’a, kamar yadda NCDC ta bayyana.

    Jimillar mutum 205,926 cutar ta shafa a Najeriya yayin da ta kashe mutum 2,723.

    Ga jerin jihohin da aka samu ƙarin cutar:

    Lagos-45

    Kaduna-32

    Ondo-28

    Kwara-12

    Rivers-11

    Edo-8

    Ekiti-5

    Niger-5

    Zamfara-5

    Plateau-4

    Nasarawa-3

    FCT-2

    Oyo-1

  2. Maraba

    Muna maku maraba da kasancewa da mu a wannan shafin inda za mu kawo labarai da rahotanni kai tsaye kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da sauran sassan duniya.

    Sai ku kasance da mu