'Yan sanda sun kama mutum uku da ake zargi da sace dalibai a Kaduna
'Yan sanda a Najeriya sun ce sun cafke mutum uku da ake zargi su na da hannu a sace sama da dalibai 120 na wata makaranta da ke jihar Kaduna a arewa maso yammacin kasar.
Akallah 'yan bindiga ashirin da biyar ne suka sace daliban makarantar Bethel Baptist a watan Yuli da ya wuce.
A ranar lahadi 20 daga cikin daliban da ake tsare da su suka kubuta, sai dai har yanzu, 'yn bindigar na ci gaba da rike dalibai 20 a hannunsu.
Rahotanni sun bayyana cewa. Iyayen yaran sai da suka biya kudin fansa kafin a sake su, ko da yake ba a bayya ainahin adadin abin da suka ba da ba.