Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Mun kashe tirliyan 8.9 kan manyan ayyuka a 2020 - Osinbajo

Wannan shafi ne da ke kawo maku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran kasashen duniya

Rahoto kai-tsaye

Imam Saleh and Buhari Muhammad Fagge

  1. 'Yan sanda sun kama mutum uku da ake zargi da sace dalibai a Kaduna

    'Yan sanda a Najeriya sun ce sun cafke mutum uku da ake zargi su na da hannu a sace sama da dalibai 120 na wata makaranta da ke jihar Kaduna a arewa maso yammacin kasar.

    Akallah 'yan bindiga ashirin da biyar ne suka sace daliban makarantar Bethel Baptist a watan Yuli da ya wuce.

    A ranar lahadi 20 daga cikin daliban da ake tsare da su suka kubuta, sai dai har yanzu, 'yn bindigar na ci gaba da rike dalibai 20 a hannunsu.

    Rahotanni sun bayyana cewa. Iyayen yaran sai da suka biya kudin fansa kafin a sake su, ko da yake ba a bayya ainahin adadin abin da suka ba da ba.

  2. Maraba

      • Marubuci, Imam Saleh
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, BBC Hausa

    Barkanku da kasancewa da mu a wannan shafin, wanda ke kawo maku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da makwabtanta kamar Nijar da Kamaru da Ghana da ma sauran kasashen duniya.

    Sunana Imam Saleh, da fatan za ku kasance da mu tsawon wannan rana.