Ina fargabar za a ci gaba da rasa rayuka a Afghanistan - Joe Biden

Asalin hoton, AFP
Shugaba Joe Biden na Amurka ya ce yana fargabar za a sake samun asarar rayuka a yunkurin da kasarsa ke yi na kwashe Amurkawa da 'yan Afghanistan da suka yi musu aiki.
Sai dai ya ce duk da haka za su dage su ga sun kammala aikin jigilar nan da kwana 10 kamar yadda aka tsara.
Wakiliyar BBC ta ce wasu ƙawayen Amurka sun soki Joe Biden kan yadda ya yi gaggawar kwashe sojojin kasar daga Afghanistan, amma a martaninsa ya ce babu wanda ya fi su sanin abin da ya kamata su yi.
Rahotanni sun ce jiragen sojin Amurka uku sun ɗauki wasu Amurkawa a wajen filin jirgin saman Kabul, wadanda turmutsutsi bai bari sun shiga filin jirgin ba.

