'Yan kasuwa uku sun mutu a rikici da jami'an rundunar saman Najeriya a Legas

Asalin hoton, TWITTER
Wani rikici tsakanin jami'an rundunar sojin saman Najeriya da ''yan jagaliya' a Legas ya yi sanadiyyar mutuwar 'yan kasuwa uku a Legas.
Mutane da yawa sun samu raunuka a rikicin da aka yi a kasuwar Ladipo da ke unguwar Mushin a jihar ta Legas ranar Talata.
Rahotanni sun bayyana cewa rikicin ya tursasa wa 'yan kasuwa rufe sana'o'insu.
Kawo yanzu ba a san dalilin aukuwar rikicin ba,amma wasu da suka shaida lamarin sun ce sojoji da 'yan sanda sun mamaye kasuwar kuma sun dakile tashin hankalin.


