'Yan tawaye sun 'fille kan sojojin Kamaru' biyu

Asalin hoton, Getty Images
Wani hari da 'yan tawaye suka kai ya kashe sojojin Kamaru biyu tare da fille musu kai, a cewar gwamnatin ƙasar.
An ga gawarwakinsu da safiyar Laraba a Babadjou, wani gari da ke maƙotaka da yankin Arewa maso Yammacin Kamaru - ɗaya daga cikin garuruwa biyu da 'yan tawaye ke son ɓallewa.
Magajin Garin Babadjou, Gisèle Tsangue, ya ce 'yan tawaye ne suka kai harin a kan wani wurin duba ababen hawa sannan kuma wani ɗan sanda ɗaya ya ɓata.
Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) ta ce an kashe mutum aƙalla 3,500 a yankin rainon Ingila da ke Arewa maso Yamma da kuma Kudu maso Yamma tun da 'yan tawaye suka fara fafutikar a 2016.
'Yan gwagwarmaya a yankin Ingilishi na zargin ɓangaren Faransanci mafiya rinjaye da tauye su.











