Yadda aka yi mukabala tsakanin Sheikh Abduljabbar da Malaman Kano

Wannan shafin na kawo maku bayanai kai tsaye daga zauren muƙabala da gwamnatin Kano ta shirya tsakanin Malam Abduljabbar da malaman Kano

Rahoto kai-tsaye

Awwal Ahmad Janyau

  1. Malaman Kano da za su yi muƙabala da Sheikh Abduljabbar

    Kano

    Gwamnatin Kano ta bayyana mutum huɗu da za su yi muƙabala da Sheikh Abduljabbar Nasir Kabara

    Malaman sun haɗa da Dr Rabiu Umar Rijiyar Lemo da Mallam Kabiru Bashir da Mallam Abubakar Madata da Mallam Masud Hotoro.

    An kuma bayyana Farfesa Salisu Shehu shugaban cibiyar harakokin addini ta Jami’ar Bayero a matsayin alkalin mukabalar

    Sauran malaman da suka halarci muƙabalar sun hada da Shehi Bakari da Dr Saidu Dukawa da Malam Mai Bushara

  2. Sheikh Abduljabbar ya isa wurin mukabala a Kano

    Sheikh Abduljabbar Nasir Kabara ya isa wurin da gwamnatin Kano ta shirya yin makabala tsakanin shi da wasu malaman Kano.

    An shirya makabalar ne da kan tuhumar da wasu malaman Kano suke yi wa Sheikh Abduljabbar a kan zargin cin zarafin Manzon Allah (SAW) da Sahabbansa. Zargin da ya musanta.

    Gwamnatin jihar Kano ba ta bayyana sunayen malaman da za su fafata da Sheikh Abduljbbar Kabara ba a wannan mukabalar.

    Kwamishinan Al'amuran Addinai na jihar Muhammad Tahar Adamu (Baba Impossible) ya ce sai a wajen mukabalar ne za a fadi sunayen malaman da za su yi.

    Tuni Sheikh Abduljabbar ya isa wurin mukabalar. Kuma wakilin BBC ya ɗauko hoton bidiyonsa a harabar wurin mukabalar

    Sheikh Abduljabbar
  3. Ƙarin mutum 186 sun kamu da korona a Najeriya

    Hukumar daƙile cutuka masu yaɗuwa ta NCDC a Najeriya ta ce an samu ƙarin mutum 186 da suka kamu da korona a ranar Juma’a.

    Alƙalumman hukumar sun nuna cewa mutum 175 cutar ta kama a jihar Legas

    A jihar Rivers kuma cutar ta kama ƙarin mutum 8, yayin da kuma aka samu ƙarin mutum uku a jihar Gombe.

    Kusan kwana biyar cutar ba ta yi kisa ba a Najeriya. Jimillar mutum 2,122 cutar ta kashe a Najeriya

    NCDC

    Asalin hoton, NCDC

  4. Maraba

    Muna maku maraba da kasancewa da mu a wannan shafin inda za mu kawo labarai da rahotanni kai tsaye kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya.