'An kusa cimma matsaya kan yarjejeniyar nukiliyar Iran'

Asalin hoton, AFP
An kammala tattaunawa kan ƙoƙarin farfaɗo da yarjejeniyar nukiliyar Iran ta shekarar 2015 a Vienna, inda mahalarta taron suka ce an samu ci gaba sosai.
Jami'in Tarayyar Turai wanda ke jagorantar tattaunawar, Enrique Mora, ya ce yana da yaƙinin za a cimma yarjejeniya ta ƙarshe.
Wakilin Rasha, Mikahil Ulyanov, ya ce yana ganin an kusa cimma yarjejeniya.
An yi tattaunawar da nufin ganin Amurka ta sake shiga yarjejeniyar yayin da Iran za ta ci gaba da cika alkawuranta na nukiliyar, waɗanda suka haɗa da daina inganta makamashin uranium.


















