Tsohuwar Ministar Mata Aisha Alhassan ta rasu

Wannan shafi ne da ke muku labarai da rahotanni kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail and Buhari Muhammad Fagge

  1. Ƙarin mutum 28 sun kamu da korona a Najeriya

    Korona

    Asalin hoton, Getty Images

    Ƙarin mutum 28 sun kamu da cutar korona a Najeriya ranar Alhamis, a cewar hukumar yaƙi da yaɗuwar cutuka ta ƙasar, NCDC.

    Bisa alƙaluman da ta wallafa, sabbin kamuwar sun fito ne daga jihohi shida na ƙasar har da Abuja.

    Jihohin su ne: Legas (10), Rivers (7), Akwa Ibom (7), Delta (2), Abuja (2), Kaduna (1).

    Ya zuwa yanzu, jumillar mutum 165,301 ne suka kamu da cutar a Najeriya, 2,065 sun mutu da kuma 155,424 da aka sallama bayan sun warke.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  2. Marabanku

    Barkanmu da sake haɗuwa a shafin labarai kai-tsaye na BBC Hausa, wanda zai kawo rahotannin abubuwan da ke faruwa a sassan duniya, musamman a Najeriya da Nijar da maƙotansu.

    Umar Mikail ne ke tare da ku a wannan hantsi na Juma'atu babbar rana.