Ƙarin mutum 28 sun kamu da korona a Najeriya

Asalin hoton, Getty Images
Ƙarin mutum 28 sun kamu da cutar korona a Najeriya ranar Alhamis, a cewar hukumar yaƙi da yaɗuwar cutuka ta ƙasar, NCDC.
Bisa alƙaluman da ta wallafa, sabbin kamuwar sun fito ne daga jihohi shida na ƙasar har da Abuja.
Jihohin su ne: Legas (10), Rivers (7), Akwa Ibom (7), Delta (2), Abuja (2), Kaduna (1).
Ya zuwa yanzu, jumillar mutum 165,301 ne suka kamu da cutar a Najeriya, 2,065 sun mutu da kuma 155,424 da aka sallama bayan sun warke.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X
