An kawo ƙarshen matsalar ruwan famfo a Abuja

Asalin hoton, Getty Images
Hukumomi a birnin Abuja, babban birnin Najeriya sun ce sun kawo ƙarshen matsalar ruwan famfo da ta addabi wasu sassa na birnin bayan tsawon kwana 12.
Unguwannin da lamarin ya fi shafa sun haɗa da Ushafa da Kubwa da Dutsen Alhaji da Katampe da wasu sassa na Jabi da Gwarinpa da wasu sassan Garki.
Lamarin ba ƙaramin sanya mutanen yankunan cikin tasku ya yi ba, musamman waɗanda ba su da rijiyoyin burtsatse.
Wasu mazauna yankunan sun tabbatar wa da BBC cewa yanzu sun samu ruwan bayan kusan mako biyu.
- Kuna iya karanta taskun da mazauna birnin suka shiga a nan
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X




