'Saudiya na min barazana kan binciken kisan Jamal Khashoggi'

Asalin hoton, Google
Ofishin hukumar kare hakkin dan adam ta Majalisar Dinkin Duniya ta tabbatar da wani bayani da kwararriyar da ke jagorantar binciken kwakwaf kan kisan dan jaridar nan na Saudiyya Jamal Khashoggi, na zargin cewa wani babban jami'in Saudiyya ya yi mata barazana ga rayuwarta.
Kakakin hukumar Rupert Colville ya tabbatar da cewa bayanan da aka wallafa a jaridar Guardian gaskiya ne kan baranar da aka yi wa Agnes Callamard, cikin wani sakon email da aka turawa kamfanin dillancin labarai na Reuters.
A ranar Talata ne jaridar Guardian ta ruwaito Callamard na cewa wani babban jami'in Saudiyya ya mata barazanar cewa za a yi maganinta matukar "ba ta dakata da" gudanar da bincike ba kan kisan da aka yi wa dan jaridar.
Colville ya kara da cewa ofishin ya sanar da Callamard cewa hukumomi da kuma bangaren tsaro na MDD na sane da abin da ya faru.

