Atiku ya soki yadda gwamnatin Najeriya ke kashe kuɗaɗe a wasu ayyuka

Wannan shafin na kawo maku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da makwabtanta da sauran ƙasashen duniya.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail and Umaymah Sani Abdulmumin

  1. Mutuwar Magufuli: An ɗauke tauraruwa mai haske daga Afirka - Goodluck Jonathan

    Goodluck Jonathan

    Asalin hoton, @GEJonathan

    Tsohon Shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ya yi alhinin rasuwar shugaban Tanzania John Magufuli, yana mai bayyana shi da "abokin dimokuraɗiyya" kuma "ɗan kishin ƙasa wanda ya so ƙasarsa".

    Jonathan ya miƙa ta'aziyyar ne a shafinsa na Twitter. "An ɗauke wata tauraruwa mai haske daga Nahiyar Afirka," in ji Jonathan.

    A jiya Laraba shugaban ya mutu sakamakon ciwon zuciya kuma nan gaba a yau za a rantsar da mataimakiyarsa Samia Suluhu domin shugabantar Tanzania.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  2. Shugaban Uganda Museveni na alhinin mutuwar shugaban Tanzania

    Shugaban Uganda Yoweri Museveni ya bayyana marigayi John Magufuli a matsayin "mai ƙarfin zuciya wanda ya duƙufa wajen haɓaka tattalin arzikin al'ummar Gabashin Afirka".

    Cikin wani saƙon Twitter da ya wallafa, shugaban ya miƙa ta'aziyya ga 'yan Tanzania.

    "Mun bi sahun 'yan Tanzania wajen yin makokin mutuwar ɗa ga Afirka," a cewarsa.

    Mista Magufuli ya mutu ne da yammacin Laraba a asibitin Mzena da ke babban birnin ƙasar, Dar es Salaam, sakamakon ciwon zuciya.

    Ya shafe fiye da shekara 10 yana fama da larurar.

    Matamakiyar shugaban, Samia Suluhu, ta ce a ranar 14 ga watan Maris ne jikin shugaban ya yi tsanani kuma aka kwantar da shi a asibiti.

    Anjima a yau Alhamis ake sa ran za a rantsar da ita a matsayin shugaba mace ta farko a ƙasar sannan kuma mace ta farko Musulma a matsayin shugabar ƙasa a Afirka.

    • Tarihin mace ta farko da za ta zama shugabar kasar Tanzania bayan mutuwar John Magufuli
    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  3. Gwamna Masari ya caccaki Sheikh Gumi kan yi wa 'yan fashi afuwa

    Aminu Bello Masari

    Asalin hoton, @GovernorMasari

    Gwamnan Jihar Katsina da ke arewa maso yammacin Najeriya, Aminu Bello Masari, ya nuna rashin goyon bayansa game da shirin neman afuwa da Sheikh Ahmad Gumi yake so gwamnatoci su yi wa 'yan fashin daji.

    Da yake magana ta kafar talabijin ta Channels a yammacin Laraba, Masari ya nuna cewa "babu abin da malamin addinin ya sani" game da yunƙurin gwamnonin yankin a yaƙi da 'yan fashin.

    "Yana wurin ne? Me ya sani game da abin da muka yi a Kaduna? Na ƙalubalanci Gumi ya fito ya faɗa mana abin da ya san mun aiwatar a Kaduna," a cewar Masari, yayin da yake martani game da ra'ayin Gumi kan salon gwamnoni a yaƙi da ɓarayin.

    Yayin zagayen da Ahmad Gumi yake yi a cikin daji domin yi wa 'yan fashin wa'azi, malamin ya ce mutanen sun faɗa masa cewa jami'an tsaro sun kashe musu 'yan uwa da ƙwace musu dukiyoyi, abin da ya sa suka ɗauki makamai kenan.

    Masari ya ce: "Abubuwan da suke faɗa masa (Gumi) a yanzu tun 2015 suke faɗa, shi suka faɗa a 2019. Me ya sani game da dazuka? Ko dai yana tausaya wa miyagu ne?"

    Kazalika, gwamnan ya ce ba ya goyon bayan yunƙurin da malamin yake yi na shiga tsakanin gwamnoni da kuma masu aikata kashe-kashen da sace mutane domin neman kuɗin fansa.

    Masari ya ce abin da 'yan bindigar ke buƙata shi ne wa'azi da gyaran tarbiyya domin su gane munin abin da suke aikatawa na kashe-kashen mutane.

    Kawo yanzu, kusan ɗalibai 800 aka sace tun watan Disamba a jihohin Kaduna da Zamfara da Neja da Katsina daga makarantunsu.

  4. 'Yan gudun hijira 100 sun kamu da korona a Kamaru

    'Yan gudun hijira

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar kula da 'yan gudin hijira a Kamaru ta nuna fargaba game da bullowar annobar korona a sansanonin 'yan gudun hijira.

    Bisa alƙaluman da ta wallafa, hukumar ta ce fiye da mutum 100 annobar ta kama zuwa yanzu, lamarin da ta ce ya kamata ta tashi tsaye domin shawo kan yaɗuwar cutar.

    Sakamakon haka ne ya sa hukumar ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta miƙa wa ma'aikatar kiwon lafiya tallafin wasu kayayyaki da ake buƙata domin bai wa waɗanda suka harbu da cutar ɗauki a asibitocin da ake kula da su.

    Ana ƙiyasta adadin 'yan gudun hijira da suke rayuwa a sansanoni a Kamaru sun kai fiye da 430,000 a yanzu haka.

  5. Rasha ta kira jakadanta a Amurka zuwa gida

    Putin da Trump

    Asalin hoton, Reuters

    Rasha ta kira jakadanta a Amurka domin tattaunawa yayin da take kokarin kare abin da ta kira tabarbarewar dangantaka da ba za a iya gyarawa ba da Amurkar.

    Cikin wata sanarwa, ma'aikatar harkokin wajen Rasha ta zargi Amurka da kokarin kawo karshen alakarsu a shekarun baya-bayan nan.

    Matakin ya biyo bayan wani rahoton sirri na Amurka da ya zargi Rasha da kokarin yin katsalandan a zaben da ya bai wa Shugaba Biden nasara - abin da Rashar ta musanta.

    Mista Biden ya gargadi Shugaba Putin cewa Amurka za ta dauki mataki.

  6. Ƙarin mutum 187 sun kamu da cutar korona a Najeriya

    Rigakafin korona

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukuma mai yaƙi da cutuka masu yaɗuwa a Najeriya NCDC ta ce mutum 187 ne suka kamu da cutar korona a ƙasar ranar Laraba.

    Cikin sabbin alƙaluman da ta wallafa a shafinta na Twitter, NCDC ta ce an samu mutanen ne a jihohi guda 18, waɗanda suka haɗa da Legas mai mutum 42 da Taraba mai 29, sai kuma Edo mai mutum 17.

    Sauran su ne: Abia (13), Rivers (11), Kaduna (10), Katsina (9), Oyo (9), Kwara (7), Plateau (7), Ondo (5) Bayelsa (4), Cross River (4), Ogun (4), Osun (4), Akwa Ibom (3), Borno (3), Nasarawa (3).

    Ya zuwa yanzu, jumillar mutum 161,261 ne suka harbu da cutar a Najeriya, sai 2,027 da suka mutu sannan aka sallami 146,395 daga asibiti bayan sun warke.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  7. Assalamu Alaikum

    Barkanmu da hantsin Alhamis tare da fatan mun tashi lafiya.

    Ku biyo ni Umar Mikail domin sanin halin da duniya ke ciki, musamman a Najeriya da Nijar da maƙotansu.

    Mu je zuwa!