Mata sun fi fuskantar cin zarafi daga abokan zamansu - WHO

Wannan shafin na kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Fauziyya Kabir Tukur and Awwal Ahmad Janyau

  1. Masu zanga-zanga sun tsere wa samamen ƴan sanda a Myanmar

    Aung Saan Suu Kyi

    Asalin hoton, Getty Images

    Dubban masu adawa da sojojin Myanmar sun ce sun yi nasarar tserewa samamen cikin dare da jami'an tsaro suka yi a wata gunduma mafi girma a Yangon, babban birnin ƙasar.

    Masu fafutuka sun tsinci kansu a maƙale a gidajen da ke Sanchaung bayan ƴan sanda sun sanar a ranar Litinin cewa za su bi gida-gida su yi bincike don gano waɗanda ba ƴan gundumar ba.

    Sun yi gargaɗin hukunta duk wanda suka kama yana bai wa masu zanga-zanga mafaka.

    Rahotanni na cewa an tsare kimanin mutum 50.

    Majalisar Ɗinkin Duniya ta jagoranci kiraye-kirayen a dakatar da matakin.

    Wasu daga cikin waɗanda suka tsere sun yi alƙawarin ci gaba da zanga-zangar da suke yi.

  2. Mutum 371 sun kamu da cutar korona a Najeriya ranar Litinin

    Hukumar daƙile cututtuka masu yaɗuwa a Najeriya NCDC ta ce an samu ƙarin mutum 371 da suka kamu da annobar korona a ƙasar ranar Litinin, sannan 13 sun mutu.

    Bisa sabbin alkaluman hukumar, a wannan rana, jihar Legas ce ke kan gaba a jerin jihohin da aka samu ɓullar cutar da mutum 102 da aka tabbatar sun kamu da cutar.

    Alƙaluman hukumar sun nuna cewa an samu mutum 65 a Enugu, da gwajin da aka yi musu ya nuna cewa sun kamu, abin da ke nufin cewa jihar ce ta biyu a wannan rana.

    Mutum 56 sun kuma sun kamu da korona a Edo sai Birnin Tarayya Abuja da aka samu mutane 23 da aka tabbatar sun kamu da Ogun da aka samu mutum 20.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X