Buhari ya bai wa masu yi wa ƙasa hidima aikin yi da kyautar kuɗi

Wannan shafin na kawo maku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da makwabtanta da sauran ƙasashen duniya.

Rahoto kai-tsaye

Fauziyya Tukur and Umar Mikail

  1. An nuna wani bidiyo mai 'cike da hujjoji' a zaman sauraren tsige Trump

    Amurka

    Asalin hoton, EPA

    Bayanan hoto, Ɗaya daga cikin masu zanga-zangar zaune a kujerar kakain majalisar Nancy Pelosi

    An nuna wa sanatoci a zaman sauraren ƙarar tsige Donald Trump wani bidiyo mai 'cike da hujjoji' na ranar da waɗanda ake tunanin magiya bayansa ne suka afakawa majalisar dokokin Amurkar.

    Hoton bidiyon ya nuna ƴan sanda suna karawa da masu zanga-zangar kuma suna roƙon a kawo masu ɗauki.

    Ƴan sanda sun kange ƴan majalisar, a wanu lokaci ma babu tazara sosai tsakaninsu da masu zanga-zangar daf da za su auka zauren majalisar.

    Lauyoyin ƙasar sun ce Mista Trump ne ya ingiza magoya bayan nasa ta hanyar wallafa wani saƙo a shafinsa na Twitter.

    Ana buƙatar kashi biyu cikin uku na ƴan majalisar su amince da tsige Trump, amma haka zai yi wuya saboda mafi yawan ƴan Republican na nan tare da tsoho shugaban.

    Amma idan aka tsige shi, ba zai iya sake tsayawa takarar shugaba a ƙasar ba har abada.

  2. Human Rights Watch ta zargi Gwamnatin Habasha da kashe fararen hula

    Shugaba Abiy Ahmed

    Asalin hoton, Reuters

    Ƙungiyar Human Rights Watch mai fafutukar kare haƙƙin ɗan Adam ta zargi gwamnatin Habasha da jefa abubuwan fashewa a birane lokacin rikicin da aka yi a watan Nuwamba a Tigray.

    Ƙungiyar ta ce hare-haren sun saɓa wa dokokin yaƙi.

    Gwamnatin Habasha ba ta ce komai ba kan zargin amma a baya ta taɓa kare ayyukan dakarunta.

    An riƙa sa abubuwan fashewa a gidaje da makarantu da kasuwanni a hare-haren kan mai uba da wabi a yankin Tigray.

    ƙungiyar Human Rights Watch ta ce fararen hula 83 ciki har da yara ƙanana aka kashe kuma sama da 300 sun samu raunuka.

    Wannan ya saɓa kalaman Firayi minista Abiy Ahmed wanda ya yi a baya yana cewa sojojin ƙasar ba su kashe farar hula ko guda ba.

  3. Shugaban Congo-Brazzaville na neman wa'adi na huɗu

    Shugaban Congo-Brazzabille

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Shugaba Denis Sassou Nguesso ya kwashe shekaru 36 a mulki

    Hukumomi a Congo-Brazzaville sun miƙa sunayen ƴan takarar shugaban ƙasa ga kotu da amincewa da su kafin zaɓen da za a gudanar ran 21 a Maris.

    Shugaba Denis Sassou Nguesso zai fafata da ƴan takara bakwai ciki har da ministan kuɗi Mathias Dzon da Guy-Brice Parfait Kolelas ɗan tsohon shugaban firayi minista.

    Sassou Nguesso mai shekaru 77 na neman wa'adi na huɗu kuma tun a shekarar 1979 ya ke kan mulki in ban da shekaru biyar da ya yi faɗi zaɓe a 1992.

    Sauran ƴan takarar sun haɗa da Albert Oniangue, tsohon mataimakin Sassou Nguesso da Joseph Kignoumbi Kia Mbougou wani tsohon minista da Deve Mafoula wani mai shekaru 38.

  4. Sanatocin Najeriya na son a yi sauye-sauye ga rundunonin tsaron ƙasar kan matsalar tsaro

    Nigeria Police

    Asalin hoton, Getty Images

    Majalisar dattijan Najeriya ta yi kira da a yi sauye-sauye a rundunonin tsaron ƙasar don magance ƙaruwar matsalolin tsaro.

    A wani zama da suka yi, shugaban majalisar Ahmad Lawan ya buƙaci jami'an tsaro su yi amfani da jirage maras matuƙi da masu saukar ungulu a dazukan ƙasar don kamo masu aika manyan laifuka.

    Haka kuma, sanatocin sun nemi gwamnoni da su ƙara matsa ƙaimu don ganin su kawo ƙarshen rikicin manoma da makiyaya.

    A watan da ya gabata ne shugaban Najeriyar Muhammadu Buhari ya sauya manyan hafsoshin tsaron ƙasar don nuna tabarɓarewar tsaro.

  5. An gano mutum 161 masu ɗauke da Ebola a DR Congo

    Ebola

    Asalin hoton, AFP

    Hukumomin lafiya a DR Congo sun ce sun gano mutum 161 da suka yi mu'amala da matar nan da ta mutu sakamakon Ebola ran 3 ga watan Fabrairu, a ɓullar cutar ta baya-bayan nan a ƙasar.

    Ministan lafiya na yankin Nord Kivu, Eugene Nzanzu Syalita ya ce kawo yanzu ba a gano mutum biyu da ake kyautata zaton suna ɗauke da cutar ba.

    Mutuwar matar a Biena kusa da birnin Butembo a yankin Nord Kivu ya alamta ɓarkewar cutar a karo na 12.

    Ran 18 ga watan Nuwamba ne gwamnati ta sanar da ƙarshen ɓullar cutar a karo na 11 a yankin arewa maso yammacin ƙasar.

    A ƙalla mutum 2277 ne suka mutu a annobar cutar Ebola a baya, a gabashin ƙasar tun daga watan Agustan 2018 zuwa Yunin 2020.

  6. Mutum 1,131 sun kamu da cutar korona a Najeriya ranar Laraba

    Hukumar daƙile cututtuka masu yaɗuwa a Najeriya NCDC ta ce an samu ƙarin mutum 1,131 da suka kamu da annobar korona a ƙasar ranar Laraba.

    Bisa sabbin alkaluman hukumar, jihar Legas ce kan gaba a yawan waɗanda suka kamu da cutar ranar Laraba da mutum 297.

    Babban birnin ƙasar Abuja dake mataki na biyu wajen yawan masu cutar ne ya zo na biyu a jiya, da mutane 194 da suka kamu a wannan rana.

    An samu mutum tamanin da uku da suka kamu a kaduna, sai Hamsin da tara a Kano, da kuma mutane Hamsin da tara a jihar Oyo da aka tabbatar da cewa sun kamu da cutar korona a ranar Larabar.

    A jihar Taraba an gano mutane Hamsin da uku da suka kamu, sai kuma Imo da aka samu Hamsin da biyu, da wasu aarba'in da bakwai a Osun, sai kuma arba'in da biyar a Plateau.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  7. Buɗewa

    Barkanku da shigowa wannan shafin inda muke kawo maku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da makwabtanta da sauran ƙasashen duniya.

    Da fatan za ku kasance da mu daga nan har zuwa lokacin da za mu rufe shafin.