Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Korona: Kaduna ta sanar da ranakun rufe makarantu da jami'o'in jihar

Wannan shafin na kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail

  1. Sakataren Gwamnati Boss Mustapha ya killace kansa saboda korona

    Sakataren Gwamnatin Tarayyar Najeriya, Boss Mustapha, ya killace kansa bayan wasu daga cikin iyalan gidansa sun kamu da cutar korona.

    Boss Mustapha wanda shi ne shugaban kwamitin yaƙi da korona na shugaban ƙasa, ya bayyana hakan ne a jiya Lahadi cikin wata sanarwa.

    "Ina mai shaida wa al'umma cewa wasu daga cikin iyalan gidana sun kamu da korona a yammacin jiya (Asabar)," in ji sakataren.

    "Duk da cewa ba su fara nuna alamar cutar ba, an killace su kuma suna samun kulawa a ɗaya daga cikin cibiyoyin killace mutane na gwamnati.

    "Gwaji ya nuna ni da matata ba ma ɗauke da cutar amma za mu ci gaba da killace kanmu sannan mu yi aiki daga gida kamar yadda dokokin yaƙi da cutar suka tanada.

    "Ina so na tunatar da 'yan Najeriya cewa cutar korona gaskiya ce. Kamar yadda hukumar NCDC ta sanar a makon da ya gabata, ana samun ƙarin masu kamuwa da cutar a jihohi da dama."

    Kwana huɗu kenan a jere ana samun mutum fiye da 400 da ke kamuwa a kullum a Najeriya da kuma mutum bakwai da suka mutu a ranakun Asabar da Lahadi.

  2. Kwastam sun kama mota maƙare da makamai a Jihar Kebbi

    Dakarun hukumar hana fasa ƙwauri na Najeriya Kwastam sun kama wata babbar mota maƙare da bindigogi ƙirar gida a Ƙaramar Hukumar Yauri na Jihar Kebbi da ke arewa maso yammacin ƙasar.

    Hukumar ta bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da ta fitar a yammacin Lahadi, inda ta ce bindigogin da aka kama a cikin buhunhuna sun kai guda 73 da kuma harsashi 891.

    Mai magana da yawun Kwastam a Najeriya wanda kuma ya sanya wa sanarwar hannu, Joseph Attah, ya ce an kama mutum uku da ke tare da motar kuma tuni an fara bincike a kansu.

    Kwamanda mai kula da yankin na Zone B, Hamisu Albashir ya bayyana kamen da cewa "wani saƙo ne ga duk wanda ke yunƙurin shigowa da makamai cikin Najeriya ta Zone B".

    Kazalika, ya yi kira ga mazauna yankin musamman na kan iyaka da su kai wa jami'an tsaro da rahoto domin taimaka wa harkar tsaro.

  3. Yau za a fara yi wa Amurkawa riga-kafin cutar korona

    Amurka ta fara jigilar raba riga-kafin Pfizer a fadin ƙasar da nufin kawar da annobar Korona.

    Wakilin BBC ya ce gwamnatin Amurka na ƙoƙarin ganin ta yi wa kashi ɗaya bisa uku na 'yan ƙasar allurar riga-kafin a cikin wata biyar zuwa shida.

    Kashin farko na riga-kafin ya kai guda miliyan uku kuma za a fara yi wa mutane yau Litinin.

    Za a fara yi wa ma'aikatan lafiya da tsofaffi da kuma sauran marasa galihu.

    Shugaba Trump ya musanta zargin cewa shi da ma'aikatan Fadar White House ne a sahun farko na waɗanda za a fara yi wa riga-kafin.

    Kusan mutun 300,000 ne annobar cutar korona ta kashe a Amurka.

  4. Ƙarin mutum uku sun mutu a Najeriya saboda cutar korona

    NCDC, hukumar da ke aikin daƙile cutuka masu yaɗuwa a Najeriya, ta ce an samu ƙariun mutum 418 da suka kamu da cutar vkorona a ƙasar a jiya Lahadi.

    Haka nan, wasu mutum uku sun rasa rayukansu sakamakon cutar.

    Sanarwar da NCDC ta wallafa a shafinta na intanet ta ce an samu sabbin kamuwar ne a jiha 17 da suka haɗa da Legas (113) da Abuja (86) Abia (47) da Kaduna (39).

    Sauran su ne Rivers (27) da Katsina (22) da Benue (14) da Oyo (13) da Kano (12) da Enugu (8) da Edo (7) da Imo (7) da Bauchi (6) da Ebonyi (6) da Ogun (6) da Ondo (4) da kuma Nasarawa (1).

    Ya zuwa yanzu, jumillar mutum 73,175 ne suka harbu da cutar korona a Najeriya, sai 1,197 da suka mutu daga cikinsu da kuma 66,090 da aka sallama daga cibiyoyin killace masu cutar bayan sun warke.

  5. Assalamu Alaikum

    Kun shigo shafin labarai kai-tsaye na abubuwan da ke faruwa a sassan duniya, musamman Najeriya da Nijar da maƙwabtansu.

    Umar Mikail ne zai kawo rahotannin a wannan hantsi.