Kwararar 'yan gudun hijira daga Najeriya a Kamaru ta ƙara yawan yara marasa takardar shaidar haihuwa
Kwararar dubban 'yan gudun hijira daga Najeriya da maƙwabtanta zuwa cikin Kamaru sun ƙara yawan yaran da ba su da takardar shaidar haihuwa a jihohin arewacin ƙasar.
A dalilin haka ne hukumar kula da ‘yan gudun hijira (UNHCR) ta shirya wani taron wayar wa iyayen yaran kai domin kauce wa wannan lamari.
A yanzu haka rashin samar wa yara takardar shaidar haihuwa ya zama wani ƙudirin doka da ‘yan majalisar dokoki ke tattaunawa a kai domin samar da hanyoyi mafiya sauki wurin samar wa yara takardar.
Sansanin Minawawo ne ke da mafi yawan 'yan gudun hijira da ke kan iyakar Najeriya da Kamaru.
Da ma dai an daɗe ana kokawa kan yaran da ba su da takardar shaidar haihuwa a arewacin Kamaru, inda yake fama da rikicin 'yan tawaye da ke son ɓallewa daga ƙasar.