Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

RFI ta yi kuskuren wallafa labarin mutuwar Sarauniyar Ingila

Wannan shafin na kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail and Awwal Ahmad Janyau

  1. PDP ce jam'iyya mafi nagarta a Najeriya – Atiku

    Tsohon mataimakin shugaban Najeriya kuma jigo a ɓangaren adawa, Atiku Abubakar, ya yi kurarin cewa jam'iyyarsu ta PDP ce "mafi nagarta" a ƙasar.

    Atiku wanda ya yi wa PDP takarar shugaban ƙasa a zaɓen 2019, ya ce ya kamata dukkanin ɓangarorin siyasar Najeriya su zama ƙarƙashin shugabancinta "saboda ita ce jam'iyyar da ta yi amanna da ɗorewar Najeriya".

    Atiku ya bayyana haka ne a yau Litinin cikin wani saƙon Twitter da ya wallafa a shafinsa.

    "Jam'iyyar PDP na da ayyukan da za ta yi a lungu da saƙo na Najeriya kuma ina shawartar dukkanin 'yan Najeriya daga ɓangarori da su yi amanna da PDP, wadda ta yi amanna da ɗorewar Najeriya," in ji Atiku.

    Wannan batu na Atiku na zuwa ne yayin da rahotanni ke cewa kan gwamnonin jam'iyyar ya rabu game da wanda zai gaji Uche Secondus a matsayin shugabanta, wanda wa'adinsa ke ƙarewa a watan Disamba mai zuwa.

  2. Wata shida ba a biya sabbin 'yan sanda albashi ba a Najeriya

    Wani bincike da BBC ta gudanar a sassan Najeriya ya nuna cewa wasu 'yan sanda kusan 10,000 da aka ɗauka aiki a shekarar da ta gabata ba a biya su albashi ba.

    Tsawon wata shida ke nan, ba a fara biyansu albashi ba tun da suka kama aiki a watan Mayu.

    Hakan ya tilasta wa galibinsu zama mabarata a tsakanin jama'a domin samun abin rayuwa.

    Sai dai, wata majiya a hukumar kula da aikin 'yan sanda a ƙasar ta ce suna sane da wannan matsala kuma ana ƙoƙarin shawo kan lamarin.

    Wani da ya nemi a ɓoye sunansa ya shaida wa BBC cewa hatta a lokacin da suka kammala karɓar horo ba a ba su komai ba, "sai wasu 'yan ƙalilan daga cikimmu da suka zo daga baya".

    Latsa hoton da ke ƙasa domin sauraron rahoton Abdussalam Ibrahim Ahmed:

  3. Akwai tabbacin za a gudanar da gasar Olympics 2021 - Thomas Bach

    Shugaban kwamitin shirya wasannin Olympics na duniya - da ke ziyara a Japan - ya ce yana da tabbacin cewa za a gudanar da wasannin Olympic a Tokyo da aka ɗage a gaban 'yan kallo a baɗi.

    Thomas Bach ya ce za a yi ƙokari domin tabbatar da cewa an yi wa da dama daga cikin masu shiga gasar da ƴan kallo rigakafin korona kafin su isa Japan.

    Firaministan Japan Yoshihide Suga ya ce a shirye yake ya karbi bakwancin wasannin tun da ta tabbata cewa ana dab da kawo karshen Covid-19.

    Wakilin BBC ya ce cikin abubuwan da Mista Bach zai yi har da fatan karfafa gwiwar ƴan Japan kan muhimmancimn karbar baƙuncin gasar.

    Hakan ya samo asali ne sakamakon ra'ayoyi da ke nuna ƴan ƙasar da dama na nuna damuwa kan kuɗaɗen da za a kashe da kuma haɗarin da lafiyarsu ke iya shiga.

  4. Ƙarin mutum 152 ne suka kamu da cutar korona a Najeriya ranar Lahadi

    Hukumar daƙile cutuka masu yaɗuwa a Najeriya NCDC ta ce an samu karin mutum 152 da suka kamu da cutar korona a ranar Lahadi a ƙasar.

    Jihar Legas ce mai adadi mafi yawa da mutanen 136 da suka kamu a ranar ta Lahadi, sai Kano mai mutum 4, Neja mai mutum 3 da suka kamu a ranar ta Lahadi.

    Jihohin Ekiti da Kaduna da Ogun da kuma Taraba su kuma na da mutum 2-2 da suka kamu a kowacce jiha.

    Abuja babban birnin tarayyar Najeriya kuwa na da mutum 1 da ya kamu a ranar Lahadin.

    Da wannan sabbin alkaluman, jumillar wadanda cutar ta kama a ƙasar sun kai 65,148, an kuma sallami mutum 61,073, sai kuma mutum 1,163 da suka mutu.

  5. Assalamu Alaikum

    Barka da hantsin Litinin - Mande Tushen Aiki - sannunku da shigowa shafin labarai kai-tsaye.

    Ni ne Umar Mikail kuma zan kawo muku yadda take kasancewa a al'amura daga sassan duniya, musamman a Najeriya da Nijar da maƙwabtansu.

    Ku biyo mu.