Sansanin Minawao a arewacin Kamaru ya karbi baƙuncin sabbin ‘yan gudun hijira 6,500 a cikin wata 11.
Hukumar kula da ‘yan gudun hijira ce ta
bayyana haka, tana mai cewa akwai dalilai da dama da suka jawo ƙaruwar adadin.
Daga ciki akwai hayayyafar jariran da ake samu
akalla 30 a duki mako, da kuma halin matsatsin da tarin wasu ‘yan gudun
hijira suka fada bayan sun fice daga sansanin domin radin kansu, abin da ya sa suke sake komawa.
Hakan ya kai ga zuwa ranar 31 ga watan
Oktoban da ya shige an lissafa ‘yan gudun hijira 68,390 a sansanin na Minawao.
A 2014, 'yan gudun hijirar Najeriya 2,500 ne ke cikin sansanin na Minawao, wanda ke kan iyakar ƙasar da Kamaru.
Lamarin na ƙara ta'azzara ne a Kamaru yayin da 'yan tawayen yankin rainon Ingila ke ƙara kai hare-hare da kuma ƙungiyar Boko Haram da ke kai nata hare-haren, abin da ke sa mazauna yankunan barin mahallansu.
A watan da ya gabata ne babban kwamishinan hukumar kula da 'yan gudun hijira a Najeriya Basheer Garba Mohammed da Gwamnan Borno Borno Babagana Zulum suka kai ziyara Nijar domin dawo da 'yan gudun hijirar ƙasar gida.