''Mun ninka harajin da muke samu a jihar Kaduna''

Asalin hoton, @GOVERNOROFKADUNA
Gwamnan jihar Kaduna Nasir Elrufa'i, ya ce jihar ta tara harajin da yawansa ya kai Naira kusan Naira biliyan 45 a shekarar 2019.
Hakan na nufin cewa jihar ta samu harajin da ya haura ninki biyu na abin da ta samu a shekarar 2016, wato shekaru huɗu da suka gabata, wato Naira Biliyan 23.
Gwamnan ya wallafa hakan ne a shafinsa na Twitter, inda ya ce hakan zai bawa gwamnatinsa damar aiwatar da ayyukan raya ƙasa da jama'a za su mora.
''Muna samun ƙaruwar haraji sannu a hankali cikin shekaru hudu da suka gabata, sannan samar da tsarin asusun ajiyar bai ɗaya na VAT ya taimaka ƙwarai wajen samun wannan nasara'' in ji gwamnan.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X


















