Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Ambaliyar ruwa na barazana ga gidan Firimiyan Sudan

Wannan shafi na kawo muku bayanai kai-tsaye dangane da irin wainar da ake toyawa a fadin duniya musamman batutuwan da suka shafi Najeriya da Nijar da makwabtansu.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail and Awwal Ahmad Janyau

  1. An yi 'ruwan wata uku cikin kwana ɗaya' a Senegal

    Shugaban ƙasar Senegal Macky Sall ya ƙaddamar da shirin bayar da taimako bayan da mamakon ruwan saman da aka yi na tsawon sa'a bakwai ya jawo ambaliyar ruwa.

    Ministan harkokin ruwa ya ce an yi ruwan saman da yawanci ana mai yawa irin haka ne cikin wata uku a cikin rana guda kacal.

    Ambaliyar ta yi ɓarna sosai inda ta lalata abubuwa da dama a mafi yawan yankunan ƙasar.

    Mutum ɗaya ya ɓata a Kaolack da ke yankin tsakiyar ƙasar.

    An kashe gwamman mutane sannan dubbai kuma sun rabu da muhallansu a wannan makon sakamakon ruwan sama kamar da bakin ƙwarya da ke jawo ambaliya a wasu ƙasashen da ke yankin Sahel.

  2. Za a gudanar da gasar Olympics a baɗi 'ko da korona ko babu'

    Hukumar da ke shirya gasar Olympics - gasar guje-guje da tsalle-tsalle mafi girma a ta duniya - ta ce za a yi wasannin a shekara mai zuwa a watan Yuli ko da annobar Korona babu.

    Mataimakin hukumar ta IOC, John Coates ne ya bayar da sanarwar, inda ya ƙara da cewa za su kafa tarihin cewa gasar ta fi karfin annobar korona.

    Sai dai akwai yiwuwar a iya samun cikas wurin tafiye-tafiye daga ƙasashen duniya zuwa birnin Tokyo na Japan, inda za a gudanar da gasar.

    Da yawa daga cikin ƴan kasar ba sa goyon bayan gudanar da ita a baɗi matuƙar annobar Korona ba ta wuce ba.

  3. Sojojin Najeriya sun kashe tare da kama 'yan fashi a Jihar Benue

    Rundunar tsaro ta sojojin Najeriya ta ce ta kashe ɗan fashi guda ɗaya tare da kama guda takwas a Jihar Benue da ke tsakiyar Najeriya ranar Lahadi.

    Kazalika ta kama guda huɗu da kuma karɓe makamai a hare-hare biyu da ta kai, a cewar wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na intanet.

    Sanarwar ta ƙara da cewa dakarun rundunar Operation Whirl Stroke ne suka kai hare-haren a Dajin Guma da ke kan iyakar jihohin Benue da Nasarawa bayan samun wasu rahotannin sirri cewa 'yan fashin na zaune a wurin.

    A wani samamen na daban, sojojin sun kama wasu mutum huɗu tare da bindigogi ƙirar AK-47 Gwer a jihar ta Benue, inda suka tarwatsa sansaninsu.

  4. Indiya ta zama ta biyu a yawan masu korona a duniya

    Indiya ta sake gano mutum 90,000 da suka kamu da cutar korona cikin kwana ɗaya, abin da ya sa ta zarce Brazil a yawan jumillar waɗanda suka kamu da cutar.

    Yanzu ƙasar ta zama ta biyu a yawan waɗanda suka harbu da cutar a duniya da mutum 4,204,613.

    Mutum 71,642 ne suka mutu, wanda shi ne adadi na uku mafi yawa a duniya. Jihohi biyar ne suka fi fuskantar ƙaruwar yaɗuwar cutar.

    Ƙaruwar na zuwa ne yayin da gwamnati ke ci gaba da sassauta dokokin yaƙi da annobar domin bunƙasa tattalin arziki, yayin da miliyoyin 'yan ƙasar suka rasa ayyukansu tun bayan kulle ƙasar a watan Maris.

    A cikin kwana bakwai da suka wuce, adadin masu kamuwa da cutar na ƙaruwa, inda mutum fiye da 75,000 ke kamuwa kullum.

  5. Adadin masu kamuwa da korona a Najeriya na ci gaba da raguwa

    Hukumar daƙile cutuka masu yaɗuwa a Najeriya NCDC ta ce adadin mutanen da annobar korona ta harba a ƙasar sun kai 55,005 bayan da aka gano ƙarin mutum 100 da suka kamu da cutar ranar Lahadi.

    Ana iya cewa wannan ne adadi mafi ƙaranci na masu kamuwa da cutar korona cikin watanni masu yawa tun da annobar ta bazu cikin ƙasar.

    A cewar NCDC, an samu mutum 3 da suka mutu a ranar Lahadin, abin da ya kai adadin wadanda suka mutu a kasar saboda cutar 1057.

    Kazalika an samu karin waɗanda suka warke daga cutar su 91 a ranar Lahadi abin da ya sa a jumullar yawan mutanen da suka warke kuma aka sallame su daga asibiti ya kai 43,013.

    A ranar ta Lahadi kuma jihar Legas ce ke kan gaba a yawan wadanda suka kamu da cutar inda aka samu mutum 39, sai Abuja babban birnin ƙasar mai mutum 22.

    Jihar Kaduna ke bi ma ta da mutum 19 da suka kamu da cutar, sai Oyo mai mutum 7, Ebonyi kuma na da mutum 6 da suka kamu a ranar ta Lahadi.

    Jihar Edo kuwa na da mutum uku, amma jihohin Katsina da Ekiti da Bauchi da Nasarawa na da mutum 1-1 a kowacensu da suka kamu.

  6. Gafaranku dai masu bibiyarmu

    Maraba da shigowa shafin labarai kai-tsaye, inda za ku samu labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da Kamaru da Ghana - har ma da sauran sassan duniya.

    Umar Mikail ke muku barka da safiyar Litinin - Mande Tushen Aiki.