Kungiyar Ipman ta mayar da farashin man fetur 162

Wannan shafi na kawo muku bayanai kai-tsaye dangane da irin wainar da ake toyawa a fadin duniya musamman batutuwan da suka shafi Najeriya da Nijar da makwabtansu.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail

  1. Shugaban majalisar wakilan Najeriya zai je Ghana kan rikicin kasashen biyu

    Gbaja

    Asalin hoton, Twitter/@SpeakerGbaja

    Shugaban majalisar wakilan Najeriya Femi Gbajabiamila zai je Ghana ranar Laraba domin tattaunawa da takwaransa na kasar kan rikicin jakadancin da ke tsakanin kasashen biyu.

    Mr Gbajabiamila ya shaida wa kafofin watsa labaran Najeriya cewa babban abin da ziyararsa za ta mayar da hankali a kai shi ne batun da ya shafi lafiyar 'yan kasarsa da ke Ghana.

    Ministocin watsa labaran kasashen biyu sun yi cacar baki a kan batun inda ministan watsa labaran Najeriya Lai Mohammed ya zargi Ghana dacin zarafin 'yan Najeriya da ke kasar da rufe shagunansu da kuma fitar da su daga kasar.

    A nasa martanin, ministan labaran Ghana Kojo Nkrumah ya ce sun fitar da 'yan Najeriya daga kasarsu ne sabodaan same su da hannu wajen aikata laifuka.

    Rikicin difilomasiyya ya ta'azzara tsakanin kasashen biyu a watan jiya bayan wani dan kasar Ghana ya rufe wani ginin ofishin jakadancin Najeriya da ke Ghana.

  2. Za a sake bude makarantu a Zimbabwe nan da mako biyu

    Dalibai na shirin rubuta jarrabawa

    Asalin hoton, EPA

    Gwamnatin Zimbabwea ta sanar da cewa za ta sake bude makarantu nan da mako biyu masu zuwa ga daliban da za su rubuta jarrabawa a karshen shekara.

    Dabilan da za su zauna jarrabawar Cambridge za su koma makaranta ranar 14 ga watan Satumba.

    Kazalika daliban da ke shirin zana jarrabawar Zimbabwe school Examinations Council (Zimsec) wacce za a soma ranar 1 ga watan Disamba, za su koma makaranta ranar 28 ga watan Satumba.

    Majalisar zartarar kasar ta dauki matakin ne bayan tattaunawar da ta yi da ma'aikatar ilimi da ta lafiya.

    Ministar watsa labarai Monica Mutsvangwa ya ce mako biyu sun isa a dauki matakin hana yada cutar korona tsakanin dalibai.

    Zimbabwe ta tabbatar da cewa mutum 6,559 sun kamu da cutar korona.

    Hukumar Lafiya ta Duniya da Asusun yara na Majalisar Dinkin Duniya Unicef sun gargadi kasashen Afirka a watan jiya game da shirinsu na sake bude makarantu saboda yara na iya harbuwa da korona.

  3. Australia ta fada matsin tattalin arziki irinsa na farko a shekara 30

    A hukumance, kasar Australia ta fada halin matsalar tattalin arziki a karoan farko cikin shekaru 30.

    Tattalin arzikin kasar ya yi kasa da kaso 7 tsakanin watan Aprilu zuwa Yuni yayin da tasirin cutar korona ya soma shafarsa.

    Barkewar cutar karona karo na biyu a birnin Victoria na iya jinkirta farfadowar al'amura.

    Australia ce kasa daya tilo da ta tsallake siradin fadawa irin wannan hali, yayin gagarumar matsalar tattalin arzikin da aka fuskanta a 2008 zuwa 2009.

  4. An kwantar da tsohon shugaban Mali Keita a asibiti

    Keita

    Asalin hoton, Reuters

    Rahotanni daga Mali na cewa an kwantar da hambararren shugaban kasar a asibiti.

    Kamfanin dillacin labarai na Associated Press ya ambato majiyoyi biyu daga asibiti na cewa tsohon shugaban kasar yana samun kulawa.

    An hambarar da Ibrahim Boubakar Keita mai shekara 75 daga kan mulki ne makonni biyu da suka wuce sannan kuma aka tsare shi na tsawon kwana goma a wani sansanin soji kafin a ba shi damar walwala.

    Lokacin da ake gudanar da tattaunawar sulhu, Mr Keita ya ce ba ya son komawa kan mulki.

    'Yan hamayya sun kwashe watanni suna kira a gare shi ya sauka daga mulki, inda suka dora alhakin tabarbarewar tattalin arziki da tsaro, da kuma cin hanci da rashawa a kansa.

  5. Maraba da shigowa shafin labarai kai-tsaye

    Barkanku da safiyar Talata, da fatan an tashi lafiya.

    Umar Mikail ke cewa ku biyo mu domin sanin yadda duniya ke ciki musamman a Najeriya da Nijar da Kamaru da Ghana.

    Kuna iya tarawa a shafukammu na zumunta wato Twitter da Facebook da Instagram domin bayyana ra'ayoyinku da kuma kallon hotuna da bidiyo.