An ceci mutumin da aka ɗaure shekaru 30 a Kano

Wannan shafi na kawo muku bayanai kai-tsaye dangane da irin wainar da ake toyawa a fadin duniya musamman batutuwan da suka shafi Najeriya da Nijar da makwabtansu.

Rahoto kai-tsaye

Awwal Ahmad Janyau and Mustapha Musa Kaita

  1. Mataimakiyar shugaban Zambia ta kamu da korona

    Mataimakiyar shugabar Zambiya Inonge Wina gwaji ya tabbatar da tana ɗauke da cutar korona.

    Ƴarta ma da suke tare ta kamu da cutar kamar shugaba Edgar Lungu ya tabbatar.

    Shugaba Lungu ya yi masu fatan samun sauki a wani saƙon da ya wallafa a Twitter.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

    Zuwa yanzu mutum 10,218 aka tabbatar da cutar korona ta shafa a Zambia.

    Hukumar kwallon Zambia ta dakatar da wasannin lig din kasar a watan da ya gabata saboda yaɗuwar cutar korona.

  2. Me zai faru bayan juyin mulkin Mali?

    Rikicin Mali

    Asalin hoton, Getty Images

    Hamɓarar da shugaba Ibrahim Boubacar Keïta ya haifar da fargaba kan makomar siyasar ƙasar Mali.

    Ƙasashen duniya da dama sun yi allawadai da juyin mulkin, inda ake bayyana damuwa kan yiyuwar ƙazancewar rikici a Mali, wadda tuni ta ke fama da rikin mayaƙa masu da'awar jihadi da kuma rikicin ƙabilanci.

    Sojojin da suka jagoranci juyin mulkin sun sanar da kafa kwamitin da zai tsara mayar da mulki ga farar hula sannan sun nuna cewa ba za su dawwama ba akan mulki.

    Amma tambayar a nan ita ce, yaushe za a gudanar da zaɓe kuma wace rawa ƴan siyasa za su taka a wajen sauya gwamnatin?

    Shugabannin ƙasashen Ecowas tuni suka mayar da hankali kan rikicin Mali inda suka fito da kuɗiri na kafa gwamnatin haɗaka domin magance rikicin siyasar ƙasar.

    Ƴan adawa sun yi watsi da wannan buƙatar inda suka jaddada lalle zai shugaba Ibrahim Boubacar Keïta da Firaminista sun yi murabus.

    Sojoji sun hamɓarar da shugaban ne ranar Talata inda suka yi amfani da buƙatar Ecowas na sanar da cewa za su kafa gwamnatin riƙon ƙwarya.

    Ko wa zai jagoranci gwamnatin riƙon ƙwarya da sojoji ke magana? Soja ko kuma wani ɗan siyasa? ko wani daga ƙungiyoyin farar hula? Tambayoyi da babu amsarsu har yanzu.

    Domin ƙarin bayani sai a karanta cikakken labarin a nan

  3. An bai wa Jagoran adawar Rasha Alexei Navalny 'guba'

    Alexei Navalny

    Asalin hoton, Reuters

    Jagoran adawa a Rasha Alexei Navalny an kwashe wshi zuwa asibiti yayin da ake zargin guba ya sha, kamar yadda mai magana da yawunsa ta bayyana.

    Navalny mai fafutikar yaƙi da rasha ya kamu da rashin lafiya ne a cikin jirgi kuma nan take jirgin ya yi saukar gaggawa a Omsk, kamar yadda Kira Yarmysh ta bayyana tana mai cewa suna zargin an barbaɗa masa guba ne a shayi.

    Wasu majiyoyi daga asibitin sun tabbatar da cewa ana ba shi magunguna ne na maganin guba.

    Mista Navalny, mai shekara 44, babban mai sukar shugaba Vladimir Putin ne.

    A watan yuni ya bayyana kuri'ar raba gardama kan yi kundin tsarin mulki garanbawul a matsayin juyin mulki wanda ya saba wa kundin tsarin mulki, sabon tsarin da zai ba shugaba Putin karin wa'adi biyu na shugabanci.

  4. Buɗewa

    Barkarmu da safiya da fatan mun tashi lafiya

    Muna maku maraba a wannan shafin da zai riƙa kawo labarai kai-tsaye a tsawon yau Alhamis game da abubuwajn da suke faruwa a duniya.