Boko Haram za ta ci gaba da yin ɓarna – Idriss Deby

Wannan shafi na kawo muku bayanai kai-tsaye dangane da irin wainar da ake toyawa a fadin duniya musamman batutuwan da suka shafi Najeriya da Nijar da makwabtansu.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail and Awwal Ahmad Janyau

  1. Gobara ta tashi a Gandun Namun Daji a Kenya

    Wata gagarumar gobara ta lalata wasu bangarori na Gandun Namun Dajin Tsavo a Kenya cikin makonnin da suka gabata, al'amarin da ya sanya rayuwar dabbobin wajen cikin hadari da kuma lalata muhalli.

    Wutar ta baya-bayan nan ta tashi ne a karshen makon nan kuma hukumar gandun daji ta Kenya KWS, ta ce wasu ne suka ta da wutar ba bisa ka'ida ba.

    Hukumomi sun tura sojoji don taimakon 'yan kwana-kwana da ke kokarin kashe wutar. Sojojin na amfani da helikwafta don zuba wa wutar ruwa daga sama.

    An kira daruruwan masu aikin sa kai daga yankunan da ke kusa da wajen don su taimaka wajen kashe gobarar.

    A wata sanarwa hukumar KWS ta ce 'yan sanda na kokarin gano wadanda suka tayar da wutar.

    An shafe makonni wutar na ci gaba da ruruwa a lokacin bazara.

    KWS ta wallafa wani hoto a wani sakon tuwita da ke nuna masu aikin sa kai na kokarin kashe wutar:

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  2. Masu aikin sa kai na aikin kare malalar man fetur a Mauritius

    Masu aikin sa kai na aikin kare malalar man fetur a Mauritius

    Asalin hoton, EPA

    Masu aikin sa kai a kasar Mauritius na ta kokarin samar da kariya don hana mai kwarara daga wani jirgin kasa daga tsibirin.

    An yi amannar jirgin dakon man na MV Wakashio wanda ke da tan 4,000 na man fetur ya kauce hanya a Tekun Indiya ranar 25 ga watan Yuli.

    Mazauna yankin suna ta shimfida buhunhuna da ledoji don kokarin hana man ci gaba da malala.

    Wasu hotuna da aka wallafa a shafukan sada zumunta sun nuna yadda masu aikin sa kai suke tattara tsinkayen shan lemo suna dinke buhunhuna da su don yin iyaka.

    Sai dai abin da suke yi din ya kauce wa umarnin gwamnati da ke umartar mutane su bar wajen don mahukunta su yi aikin tsaftace shi.

    Wani mai rajin kare muhalli ya shaida wa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa: '' Mutane suna son yin abub da kansu, mu kuma muna son kare kowa daga hadari.''

  3. Kwana 101 kenan babu wanda ya kamu da korona a cikin New Zealand

    New Zealand

    Kwana 101 kenan a jere ƙasar New Zealand ba ta samu wanda ya kamu da cutar korona ba a cikin ƙasar.

    Firaminista ƙasar Jacinda Ardern ta bayyana nasarar a matsayin gagarumin cigaba. An sha yabon salon yaƙi da cutar da ƙasar ta bi.

    Mutum 21 da ke jinyar cutar a ƙasar sun shigo da ita ne daga ƙasashen waje kuma suna killace yanzu haka.

    New Zealand ta yi ƙoƙari fiye da sauran ƙasashe, inda ta tabbatar da samun mutum 1,219 da kuma 22 da suka mutu tun daga sanda cutar ta ɓulla a ƙarshen watan Fabarairu.

  4. Gwamnatin Kamaru ta zaɓi kamfanonin da za su samar mata da man fetur

    Kamaru

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumomi a Kamaru sun zaɓi wasu kamfanoni biyu na ƙasar Switzerland da suka ci kwangilar shigowa da tataccen man fetur.

    Waɗannan kamfanoni su ne Mocoh da Trafigura.

    Kwamitin kula da samar da man fetur ne ya tantance jerin kamfanonin da suka yi zawarcin neman cin kwangilar da hukumomi suka sanar ranar 17 ga watan Yuli.

    Ana sa ran cewa za su shigo da tan 465000 na mai.

  5. Wani mutum zai kai matarsa kotu don ta yi masa leƙen asiri a WhatsApp

    Whatsapp

    Asalin hoton, Getty Images

    Wani mutum a Saudiyya na duba yiwuwar kai matarsa ƙara kotu saboda tana yi masa leƙen asiri kan saƙwanninsa na WhatsApp har tsawon wata tara.

    Jaridar Saudi Gazetteta rawaito cewa mutumin ya gano matar tasa ne, wadda malamar makaranta ce, ta shiga WhatsApp ɗinsa sannan ta sauke dukkanin saƙwanninsa tare da hotuna da bidiyo ba tare da saninsa ba.

    Mutumin ya bayyana abin da matar tasa ta aikata a matsayin leƙen asiri da kuma zamba ta intanet. Sai dai ya zaɓi a sasanta batun cikin lumana duk da girman laifin da aka aikata masa.

    A gefe guda kuma, matar ta nemi ya sake ta sannan ta nemi ya fayyace kuɗaɗen tallafi da zai ba ta kafin karɓar takardar sakin.

    A lokacin da Saudi Gazette ta tuntuɓi matar ba ta ce komai ba kan batun. Amma ta tabbatar da cewa ta nemi a raba auren saboda haka ba ta son ta bayyana sirrin aurensu a bainar jama'a.

  6. An kashe mutum ɗaya tare da jikkata aƙalla 20 a Amurka

    AMurka

    Asalin hoton, Getty Images

    ‘Yan sanda a birnin Washington-DC sun ce an harbe wani matashi, tare da jikkata aƙalla mutum 20 bayan da wasu ‘yan bindiga suka buɗe wuta a kan wani taron jama'a.

    Shugaban ‘yan sandan birnin Peter Newsham ya ce wani jami’in‘ ɗan sanda da ya tashi daga aiki ya samu munanan raunuka.

    Ya ce an riƙa buɗe wuta kan mai uwa da wabi daga ɓangarori daban-daban, kuma a yanzu ana neman aƙalla mutum uku.

  7. Assalamu Alaikum

      • Marubuci, Umar Mikail

    Kun shigo shafin labarai kai-taye na bbchausa.com. Jama'a barkammu da safiyar Litinin - tushen aiki.

    Umar Mikailne zai kasance da ku domin kawo muku labaran irin abubuwan da ke faruwa a sassan duniya musamman Najeriya da makwabtanta.

    Ku biyo mu kawai.