Ba lallai a samu riga-kafin korona a 2020 ba – WHO

Wannan shafi na kawo muku bayanai kai tsaye dangane da irin wainar da ake toyawa a fadin duniya musamman batutuwan da suka shafi Najeriya da Nijar da makwabtansu.

Rahoto kai-tsaye

Nasidi Adamu Yahaya and Mustapha Musa Kaita

  1. Rufewa

      • Marubuci, Mustapha Musa Kaita
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, Multi-Media Broadcast Journalist

    Masu bibiyarmu a wannan shafin a daidai wannan lokaci muka kawo ƙarshen kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye a wannan shafin, sai kuma gobe Asabar idan Allah ya kai mu za mu ci gaba da kawo muku wasu labaran.

    Ga wasu daga cikin labaran da muka wallafa a wannan shafin a yau:

    • WHO ta nemi jiragen sama su dauki matakan kariya
    • Shugaban ma’aikatan gidan gwamnatin Filato ya kamu da cutar korona
    • COVID-19: Minista ya sauka daga mukaminsa a Ghana
    • 'Maganin Madagascar na Maleriya ne'
    • An soma shari'ar Khashoggi a Turkiyya
    • Dan achaba ya mutu bayan ya cinna wa kansa wuta
    • Coronavirus: An kori ministan da ya karya dokar kulle
    • Mutanen da suka kamu da korona a Saudiyya sun haura 200,000
    • Gwamnan Bauchi ya dakatar da Sarkin Misau
    • An kashe sojoji tara a Mali

    Za ku iya duba ƙasa domin karanta waɗannan da ma wasu labaran.

  2. An haramta cin naman kare a wani yanki na Indiya

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    An haramta sayar da naman kare a jihar Nagaland da ke arewa maso gabashin Indiya biyo bayan kiraye-kirayen da ake yi kan lamarin.

    Cin naman kare haramun ne a wasu sassa na Indiya, sai dai wasu ƙabilu a arewa maso gabashin ƙasar na ganin cin naman kare ƙasaita ne.

    Masu kare haƙƙin dabbobi sun yi maraba da wannan yunƙuri, inda suka ce wannan babban ci gaba ne a yaƙin da ake yi da masu zaluntar karnuka.

    An yi ƙiyasin cewa a duk shekara kusan karnuka dubu 30 ake fasa ƙwaurinsu zuwa jihar Nagaland daga wasu jihohin.

    Sai dai wasu ƙungiyoyi masu zaman kansu na kallon wannan lamarin a matsayin shishigi da kuma katsalandan kan irin abincin da mutanen Nagaland ke ci.

    Ko a farkon wannan shekarar ma sai da jihar Mizoram wadda itama take a arewa maso gabashin ƙasar ta haramta sayar da naman karnuka.

  3. Kotu ta ɗaure jami'an Amnesty International biyu a Turkiyya

    Kotu ta ɗaure wasu jami`ai biyu na ƙungiyar kare haƙƙin bil`adama ta Amnesty International a kasar Turkiyya.

    An ɗaure su ne bisa kama su da laifin da ya jiɓanci ta`addanci, a wata shari`ar da ta ja hankalin ƙasashen duniya.

    Kotun, wadda ta yi zama a Istanbul ta yi wa Tan`air Kuluch ɗaurin fiye da shakara shida bisa kama shi da laifin shiga ƙungiyar ta`addanci, bayan masu shigar da ƙara sun ce yana da alaƙa da Fethulla Gulen, wani malamin addinin musulunci da ke Amurka, wanda gwamnatin Turkiyya ta ɗora masa alhakin shirya wani juyin-mulkin da bai yi nasara a shekarar 2016.

    Sai kuma ɗaya jami`in da ake kira Idil Isar da wasu mutum biyu da aka yi wa ɗaurin shekara biyu.

    Mai magana da yawun ƙungiyar Amnesty, Andrew Gardner ya bayyana shari`ar da cewa abin takaici ce ne.

  4. Ba lallai a samu riga-kafin korona a 2020 ba – WHO

    ..

    Asalin hoton, Reuters

    Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta yi gargaɗin cewa ba lallai a samu riga-kafin cutar korona a shekarar 2020 ba.

    A wata tattaunawa da 'yan jarida a Geneva, daraktan ayyukan gaggawa na hukumar Dakta Mike Ryan ya ce ko da an samu riga-kafin, babban ƙalubalen shi ne yin riga-kafin da kuma rarraba shi a farkon shekarar 2021.

    Ya bayyana cewa babbar damuwarsa ita ce ƙasashen da aka sassauta dokar kulle na yin biris da yawan ƙaruwar cutar a ƙasashen su.

    Shugaban hukumar WHO Dakta Tedros Adhanom Ghebreyesus, ya ce yana jiran sakamakon gwajin wasu magunguna da aka yi nan da makonni biyu waɗanda ake kyautata zaton za su magance cutar.

  5. Za a binciki manyan jami'an gwamnatin Faransa kan korona

    ..

    Asalin hoton, Getty Images

    Masu shigar da ƙara a Faransa za su ƙaddamar da bincike kan yadda manyan jami'an gwamnatin ƙasar suka tunkari annobar korona.

    Faransa na ɗaya daga cikin ƙasashen duniya da cutar korona ta fara kashe mutane masu ɗimbin yawa.

    Cikin waɗanda za a bincika har da Firaiministan ƙasar Edouard Philippe da kuma tsofaffin ministocin lafiya na ƙasar wato Olivier Véran da kuma Agnès Buzyn.

    Antoni Janar na ƙasar Francois Molins ne zai jagoranci binciken kuma yana da iko na gano ko an gudanar da rashin gaskiya a yaƙi da cutar korona a ƙasar.

    Sama da mutum 30,000 ne cutar ta kashe a Faransa. Ana kuma zargin gwamnatin Shugaba Emmanuel Macron da ƙarancin gwajin cutar korona ga mutane.

    Ana kuma kuma caccakar gwamnatin kan batun halin ko in kula kan batun saka takunkumi da kuma komawar ɗalibai makaranta da kuma ƙarancin kayayyakin asibiti.

  6. An kashe sojoji tara a Mali

    Wasu da ake zargin masu iƙirarin jihadi ne sun yi kwanton-ɓauna inda suka kashe sojoji tara a Mali, kwana ɗaya bayan wani hari da aka kai da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum 30 a ƙasar.

    Wani magajin gari a ƙasar ya bayyana cewa 'yan bindigar sun koma garin na Gouari da ke tsakiyar ƙasar inda suka kai hari ga sojojin kuma suka ƙona motocinsu.

    Ana samun ƙaruwar hare-hare da arangama tsakanin ƙabilun Dogon da Fulani a yankin Mopti na ƙasar Mali.

    A watan da ya gabata, Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana cewa rikici a tsakiyar ƙasar Mali a wannan shekara ya yi sanadiyar mutuwar mutum 600.

  7. Harin Bam ya jikkata mutane a Kamaru

    ..

    Mutane biyar suka jikkata a wani harin bam da aka kai a birnin Kamaru ranar Alhamis - wannan shi ne karo na uku a cikin dare hudu da ake amfani da bam din da aka haɗa na gargajiya wajen kai hari.

    Bam din ya tashi ne da misalin karfe 7:30 na dare a wani fitaccen titi kusa da inda ake sayar da burodi a birnin Yaounde.

    'Yan sanda sun ce sun yi kame, sai dai sun ƙi fadin adadin mutanen da suka kama.

    An rufe tittuna da dama sannan 'yan sanda na bin gida-gida domin bincike.

    A ranar 21 ga watan Yuni, an kai irin wannan harin a biranen Melen da Emana, wanda hakan ya haifar da fargaba sosai a zukatan mazaunan yankunan.

    Babu dai wanda ya ɗau alhakin kowanne daga cikin harin, sannan babu ƙarin bayani daga wajen jami'an 'yan sanda.

  8. Labarai da dumi-dumi, Gwamnan Bauchi ya dakatar da Sarkin Misau

      • Marubuci, Ishaq Khalid
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, BBC News, Abuja
    ..

    Asalin hoton, PM NEWS NIGERIA

    Gwamnan jihar Bauchi da ke arewacin Najeriya Bala Muhammad Kaura, ya dakatar da Sarkin Misau, Alhaji Ahmed Sulaiman sakamakon tashin hankali da aka samu a yankin tsakanin manoma da makiyaya.

    Tashin hankalin a wannan mako, a garin Zadawa da ke cikin karamar hukumar ta Misau, ya yi sanadiyyar mutuwar akalla mutum tara da jikkata wasu da dama.

    Gwamna Bala Kaura ya sanar da dakatar da Sarkin ne yayin kaddamar da wani kwamiti da zai gudanar da bincike kan rikici mai nasaba da wani fili da ake takaddama a kai.

    Gwamnan na jihar Bauchi ya kuma dakatar da wasu sarakunan gargajiya masu mukaman hakimi da dagaci a yankin da rikicin ya shafa.

    Sarkin Misau dai na daga cikin manyan sarakunan gargajiya a jihar ta Bauchi.

    Tun farko gwamnan ya dakatar da shugaban riko na karamar hukumar ta Misau da wasu manyan jami’an karamar hukumar. Gwamnatin jihar na zarginsu da yin sakaci game da rikicin.

    Gwamnan ya ce an dakatar da jami’an da sarakunan gargajiyar ne domin bayar da damar gudanar da bincike. Dakatarwar za ta ci gaba da aiki zuwa lokacin da za a kammala bincike.

    An ba kwamitin binciken da aka kaddamar makwanni uku ya gabatar da rahotonsa. Kawo yanzu ba a kai ga jin ta bakin shuwagabannin da aka dakatar ba.

    A 2015 ne dai aka nada Alhaji Ahmad Sulaiman Sarkin Misau, bayan rasuwar Sarki Muhammadu Manga.

    Ba a cika samun rikici tsakanin manoma da makiyaya a jihar ta Bauchi ba idan aka kwatanta da wasu jihohin Najeriya masu fama da irin wannan rikici da ma matsalar ‘yan bidiga.

  9. Mutanen da suka kamu da korona a Saudiyya sun haura 200,000

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    A ranar Juma'a, ƙasar Saudiyya ta bayyana cewa mutum 4,193 suka sake kamuwa da cutar korona wanda hakan ya sa jumullar waɗanda suka kamu da cutar a ƙasar ya kai 201,801.

    Jaridar Saudi Gazette ta ruwaito ma'aikatar lafiya ta ƙasar na cewa mutum 2,945 suka sake warkewa daga cutar wanda hakan ya kawo jumullar waɗanda suka warke daga cutar a ƙasar ya kai 140,614.

    Ma'aikatar ta kuma bayyana cewa mutum 50 ne suka sake mutuwa, hakan ya sa jumullar waɗanda suka mutu a ƙasar sakamakon cutar ya kai 1,802.

    Cikin waɗanda suka kamu da cutar, mutum 431 daga Dammam suke sai kuma 399 daga Al Hafouf sai 306 daga birnin Riyadh.

    Akwai kuma mutum 279 daga Al Mobarraz sai 210 a Makkah da Jeddah 169.

  10. 'Yan bindiga sun kashe 'yan sanda 8 a Indiya

    Mahukunta a ƙasar Indiya sun tabbatar da cewa wasu `yan bindiga sun kashe `yan sandan ƙasar takwas a wani kwanton-baunar da aka yi musu, lokacin da suka je kama wani da ake zargin ya aikata kisan-kai.

    Babban sifetan `yan sanda na jihar Uttar Pradesh ya ce jami`an nasu sun je kama wani gawurtaccen ɗan daba ne, mai suna Vikas Dubey, wanda manyan `yan siyasa ke ɗaure-masa-gindi, kuma ana zarginsa da kisan-kai da satar mutane da yi wa al`umma ƙwacen ƙudi.

    Ya bayyana cewa yaran ɗan daban sun hau saman rufin gida ne inda suka girke bindigoginsu, kana suka buɗe wa `yan sandan wuta.

    An dai sake tura wata rundunar `yan sandan domin su farauto `yan bindigan.

  11. Coronavirus: An kori ministan da ya karya dokar kulle

    Ghana

    Asalin hoton, AFP

    An tilasta wa mataimakin ministan harkokin kasuwanci da masana'antu a Ghana yin murabus.

    Hakan ya faru ne bayan ya saɓa umarnin killace kai duk da cewa gwaji ya nuna ya na dauke da ƙwayar cutar korona.

    Carlos Ahenkorah, wanda kuma dan majalisa ne ya ziyarci cibiyar da ake yi wa masu kada ƙuri'a rajista a yankin da ya fito na birnin Tema kafin ya cike wa'adin killace-kai.

    Sai dai a cewarsa, ya mutunta dokar bai wa juna tazara, sannan ba ya nuna alamomin cutar.

    'Yan ƙasar Ghana da dama sun buƙaci a gurfanar da shi gaban shari'a kan karya dokokin kariya da jefa rayuwar mutane a cikin haɗari.

    Akwai mutane sama da dubu 18 da suka kamu da cutar korona a ƙasashen yammacin Afirka, sama da 100 kuma sun mutu.

    Ana ci gaba da samun ƙaruwar masu kamuwa da cutar, yayin da ake sassauta dokar kulle tun a watan da ya gabata.

    Ghana na kan shirye-shiryen rungumar sabbin tsare-tsaren da ta gindaya na babban zaben kasar da ke tafe a watan Disamba.

  12. Dan achaba ya mutu bayan ya cinna wa kansa wuta

    Dan Achaba

    Asalin hoton, AFP

    Wani ɗan achaba a kasar Uganda ya mutu bayan ya cinna wa kansa wuta da nufin nuna fushinsa, bayan `yan sanda sun ƙi ba shi babur ɗinsa da suka kama.

    'Yan sanda sun ce dan achaban, mai suna Husseini Walugembe ya bai wa abokinsa ne ɗanin babur ɗin, kuma sai aka yi rashin sa`a `yan sanda suka kama shi da goyon fasinja, alhali an haramta yin haka ƙarƙashin dokokin yaƙi da cutar korona.

    An ce takaici ne ya kama dan acaban bayan ya yi ta zuwa ofishin `yan sanda domin su ba shi babur din nasa, amma suka ƙi.

    Da ya ga abin ya gagara, sai ya shiga cikin wani daki a harabar ofishin `yan sandan, kana ya kulle ya yayyafa wa jikinsa man fetur din da ya ɗura a cikin wata kwalbar ruwa, sannan ya cinna wa kansa wuta.

    `Yan sanda dai sun ce suna gudanar da bincike a kan zargin da ake yi cewa jami`ansu na karɓar cin hanci kafin su saki baburan da suka kama.

  13. An soma shari'ar Khashoggi a Turkiyya

    Jamal Khashoggi da Yarima Salman

    Asalin hoton, AFP

    An fara yin shari`a ga wasu `yan kasar Saudiyya 20 a bayan idanunsu a kasar Turkiyya bisa kisan da aka yi wad an jaridan nan Jamal Khashoggi.

    Kawarsa, Hatije Jengiz, wadda ta yi ta fadi-tashin ganin an hukunta wadanda suka kashe shi kusan shekara biyu da suka wuce, na cikin shaidun da aka fara yi wa tambayoyi.

    Ana dai tuhumar wadanda ake kara ne da yi wa Jamal Khashoggi kisan azaba da wulakanci.

    Wannan kisan yana da ban takaici da matukar tayar da hankali, kasancewar sai da aka sumar da shi kana aka daddatsa shi, kuma ana zargin wasu jami`an gwamnatin Saudiyya su 15 ne suka yi wannan aika-aikar.

    Cikin wadanda ake tuhumar, har da wasu mukarraban Yarima mai jiran gado na Saudiyya, Muhammad Bin Salman.

  14. 'Maganin Madagascar na Maleriya ne'

    ..

    Asalin hoton, AFP

    Ministan lafiya na Najeriya Osagie Ehanire ya ce maganin Madagascar wanda ake kyautata zaton yana maganin korona na da sinadare da ke magance Maleriya.

    Ministan ya bayyana cewa gwajin da aka gudanar kan maganin ya nuna cewa yana ɗauke da artemisia, wata shuka da ake amfani da ita wurin haɗa maganin Maleriya.

    Sai dai gwamnatin ta bayyana cewa tana ci gaba da gwajin maganin domin gano ko yana maganin korona.

    Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta yi gargaɗin amfani da magungunan da ba a yi gwajinsu ba domin yunƙurin magance korona.

  15. COVID-19: Minista ya sauka daga mukaminsa a Ghana

    CARLOS KINGSLEY AHENKORAH

    Asalin hoton, CARLOS KINGSLEY AHENKORAH

    An tilasta wa mataimakin ministan Ciniki da Masana'antun Ghana sauka daga kan mukaminsa ranar Juma'a.

    Carlos Kingsley Ahenkorah ya ajiye aikinsa sakamakon kin yin biyayya ga dokar killace kai bayan an tabbatar ya kamu da cutar korona, a cewar sanarwar da ofishin shugaban kasar Nana Akufo-Addo ya fitar ranar Juma'a.

    Mr Ahenkorah ya ziyarci wata akwatun yin katin zabe duk da yake ya kamu da cutar covid 19.

    Ana gudanar da aikin rijistar katin zabe a Ghana gabanin babban zaben da za a gudanar a watan Disamba.

    Mutane da dama a kasar ta Ghana sun caccaki mataimakin Ministan.

  16. Chelsea na zawarcin Digne, Manchester City na son ɗauko 'yan wasa uku

    Lucas Digne

    Asalin hoton, Getty Images

    Chelsea da Manchester City za su iya mayar da hankali kan dan wasan Everton dan kasar Faransa Lucas Digne, mai shekara 26, idan suka gaza dauko dan wasan Ingila Ben Chilwell, 23, daga Leicester.(ESPN)

    Everton,Liverpool,Manchester City da Manchester United za su kalli kwallon da Leon Bailey, mai shekara 22, zai murza ranar Asabar yayin da dan wasan na Bayer Leverkusen da Jamaica yake sha'awar komawa Ingila.(Sky Sports)

    Kocin Manchester City Pep Guardiola yana son dauko dan wasan Napoli da Senegal Kalidou Koulibaly, mai shekara 29; da dan wasan Villarreal dan kasar Sufaniya Pau Torres, mai shekara 23; da kuma dan wasan Benfica da Portugal Ruben Dias, mai shekara 23, a yayin da yake son karfafa bayan kungiyar.(Times - subscription required).

  17. Shah Rukh Khan yana alhinin rasuwar Saroj Khan

    Fitaccen tauraron fina-finan Indiya, Shah Rukh Khan, ya bi sahun sauran taurari wajen bayyana alhininsa na rasuwar shahararriyar mai fasahar rawar nan Saroj Khan wacce ta rasu ranar Juma'a tana da shekara 71.

    A wani sakon Twitter, Khan ya bayyana Saroj Khan a matsayin "malamata ta farko a masana'antar [Bollywood]. Ta shafe awanni da dama tana koya min yadda ake 'tsalle' a rawar fim," a cewarsa.

    Ya yi addu'ar Allah ya sanya ta a Aljannah.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

    Khan ta shafe kusan shekara arba'in tana sana'ar rawa, kuma ta koya wa wasu daga cikin fitattun taurarin yadda ake waka.

    Ta soma sana'ar rawa ne a shekarun 1980, inda ta yi aiki tare da fitattun taurari irin su Madhuri Dixit da Sridevi.

    Khan ta rasu ne sakamakon bugun zuciya a wani asibiti da ke Mumbai, a cewar kafofin watsa labaran kasar.

    A watan jiya aka kwantar da ita a asibiti bayan ta yi korafin cewa ba ta iya yin numfashi sosai, in ji kafofin watsa labaran Indiya.

    An yi mata gwajin Covid-19 ko da yake sakamakonsa ya nuna cewa ba ta dauke da cutar.

    Khan ta rasu ne sakamakon bugun zuciya

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Khan ta rasu ne sakamakon bugun zuciya tana da shekara 71
  18. Firaiministan Faransa ya sauka daga mulki

    Ba abin mamaki ba ne maye gurbin Firaiminista a Faransa

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Ba abin mamaki ba ne maye gurbin Firaiminista a Faransa

    Firaiministan Faransa Edouard Philippe ya mika takardar barin aikinsa bayan jagorantar gwamnatn Shugaba Emmanuel Macron kusan shekara uku.

    Ko da yake ana ganin Mr Philippe a matsayin wanda jama'a suka fi so fiye da shugaban kasa, jam'iyyar La République En Marche (Republic on the Move) mai mulkin kasar ba ta taka rawar gani ba a zabukan kananan hukumomin makon jiya.

    Shugaba Macron ya yi alkawarin fito da "sabuwar hanya" a wata hira da aka wallafa ranar Juma'a.

    Ana sa ran rushe gwamnatin nan gaba kadan, kuma ba sabon abu ba ne idan shugaban Faransa ya maye gurbin firaiminista a mulkin shekara biyar wanda aka fi sani da "quinquennat".

  19. Shugaban ma’aikatan gidan gwamnatin Filato ya kamu da cutar korona

    Noel Donjur

    Asalin hoton, Plateau state govt

    Shugaban ma’aikatan gidan gwamnatin Filato da ke Najeriya, Noel Donjur, ya kamu da cutar korona.

    Kwamishinan yada labaran jihar, Dan Manjang, ne ya bayyana haka ranar Juma'a a sakon da ya aike wa manema labarai.

    "Noel Donjur ya kamu da COVID-19 bayan umarnin da Gwamna Lalong ya bayar na yin gwaji kan mambobin majalisar zartarwar jihar ranar 1 ga watan Yuli. Sakamakon gwajin ya nuna cewa dukkansu ba sa dauke da cutar idan ban da shugaban ma’aikatan wanda bai nuna alamar kamuwa da cutar ba kuma yana cikin hali mai kyau," a cewar sanarwar.

    Mr Manjang ya kara da cewa jami'an lafiyar jihar ta Filato sun soma yi masa magani a daya daga cikin cibiyoyin kula da masu jinyar cutar da ke Jos, babban birnin jihar.

    A cewarsa, ana bibiyar mutanen da ya yi mu'amala da su ciki har da iyalansa domin yi musu gwaji.

    Kakakin gwamnatin ta Filato ya ce an yi wa wasu jami'an gwamnatin jihar gwaji, wadanda suka hada da masu taimaka wa gwamnan jihar da manyan sakatarori da shugabannin hukumomin gwamnati, kuma yanzu ana jiran sakamakon gwajin nasu.

  20. WHO ta nemi jiragen sama su dauki matakan kariya

    Jiragen sama

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumar Lafiya ta Duniya, WHO, ta yi kira ga kamfanonin jiragen saman Afirka su dauki matakan kariya a yayin da suka koma zirga-zirga zuwa kasashe daban-daban.

    WHO ta yi kira a dauki tsauraran matakai domin kauce wa yaduwar cutar korona.

    Hukumar ta kuma yi kira ga gwamnatoci su tabbatar kamfanonin jiragen samansu sun karbi bayanan fasinjoji sannan su bi kadinsu.

    Shugaban WHO reshen Afirka Dr Matshidiso Moeti ya ce sufurin jiragen sama yana da matukar amfani wajen bunkasa tattalin arziki amma halin da aka shiga yana "bukatar daukar tsauraran matakai na magance yaduwar Covid-19".

    Hukumar ta shawarci hukumomin kula da flayen jiragen sama su tabbatar fasinjoji suna dakar matakan nesa-mesa da juna, da wake hannaye da tsafta.

    WHO ta ce tuni Kamaru da Equatorial Guinea, da Tanzania da kuma Zambia suka koma jigilar fasinjoji.