'Boko Haram ta kashe sojojin Najeriya 6 a Borno'

Wannan shafi na kawo muku bayanai kai tsaye kuma da dumi-duminsu game da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya musamman masu alaka da annobar korona da ma karin wasu daban.

Rahoto kai-tsaye

Mustapha Musa Kaita and Awwal Ahmad Janyau

  1. Yawan masu kamuwa da korona na ƙaruwa a Rasha

    Kusan mutum 9,000 suka kamu da cutar korona a rana guda a ƙasar Rasha, hakan ya sa jumullar waɗanda suka kamu da cutar a ƙasar ya kai 467,673.

    Ƙasar ta kuma bayar da rahoton cewa mutum 134 suka sake mutuwa a rana guda inda jumullar waɗanda suka mutu a ƙasar ya kai 5,859.

    Ƙasar ta rasha na fama da ƙaramin matsi na tattalin arziƙi kamar yadda wasu manyan ƙasashe ke fama.

  2. Najeriya ta karɓi bashin kusan dala miliyan 300

    Bankin raya Afirka ya bai wa Najeriya rancen kusan dala miliyan 300, don taimaka mata wajen dakushe tasirin annobar korona.

    Ministar kuɗin ƙasar ta yi gargaɗi a watan jiya cewa tattalin arziƙin Najeriya mafi girma a Afirka na iya samun tasgaro da sama da kashi tara cikin 100.

    Ƙasar ta fuskanci gagarumin koma-baya sakamakon faɗuwar farashin man fetur a 'yan watannin nan.

    Ta gabatar da ƙudurin rage kuɗin da ta ware wa ɓangaren lafiya da kusan rabi, da kuma zaftare gagarumin kaso a kasafin kuɗin ɓangaren ilimi.

    Ko a watan Afrilu ma sai da Najeriya ta karɓi wani ƙunshin tallafin gaggawa na kimanin dala biliyan huɗu da miliyan 300 daga Asusun Lamuni na Duniya.

    ..

    Asalin hoton, Nigeria Presidency

  3. Korona ta sake ɓulla Sokoto da Kebbi

    ..

    Asalin hoton, Sokoto State Government

    Cutar korona ta sake ɓulla jihohin Sokoto da Kebbi da ke arewacin Najeriya bayan jihohin a kwanakin baya sun fito sun bayyana cewa an sallami duka masu cutar korona da ke a jihohin.

    A ƙididdigar da hukumar NCDC ta fitar a jiya Asabar, an samu sabbin mutum 11 da suka kamu da cutar a jihar Sokoto sai kuma mutum 2 a jihar Kebbi.

    Jihar Zamfara ce ta farko da ta fara fitowa ta bayyana masu cutar a jihar sun warke sai Kebbi sa'annan Sokoto.

    Ma'aikatar lafiya ta jihar Sokoto ta bayyana a shafinta na Twitter cewa wasu almajirai 33 da aka kai jihar daga Kaduna ne suka kai cutar Sokoto.

  4. Barkanmu da warhaka

      • Marubuci, Mustapha Musa Kaita
      • Sanya sunan wanda ya rubuta labari, Multi-Media Broadcast Journalist

    Masu bibiyarmu a wannan shafin barkanmu da wannan safiya ta Lahadi. Za mu ci gaba da kawo muku labarai da rahotanni kai-tsaye kamar yadda muka saba a wannan shafin.

    Za ku iya bin mu a shafinmu na Faceobok da Twiiter domin tafka muhawara da karanta wasu abubuwan da muke wallafawa.

    Akwai shafinmu na Instagram da za ku iya kallon hotunan da muke wallafawa, sai kuma na Youtube domin kallon wasu shirye-shiryenmu tare da kallon labaran talabijin.