Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Najeriya ta ayyana Juma'a a matsayin ranar hutu

Wannan shafi na kawo muku labarai da rahotanni kai tsaye kuma da dumi-duminsu game da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya musamman masu alaka da kisan George Floyd da annobar korona da ma karin wasu labaran.

Rahoto kai-tsaye

Nasidi Adamu Yahaya, Halima Umar Saleh and Umar Mikail

  1. Ƙasa biyar da suka fi fama da cutar korona

    Ƙasashe biyar ne suke da rabin masu cutar korona a duniya, inda a yanzu masu dauke da cutar suka haura miliyan bakwai, a cewar taswirar da Jami'ar Johns Hopkins take fitarwa.

    Amurka ce ta fi yawan masu cutar a yanzu - inda take da fiye da mutum miliyan daya da dubu 900.

    Brazil ce ta biyu inda masu cutar suka kai 700,000, sai Rasha ta uku mai mutum 467,073, Burtaniya ta hudu da mutum 287,621 sannan Indiya mai mutum 257,486.

    Amma salon yin gwaji ya bambanta a wadannan kasashe - a Amurka an samu ci gaba wajen yin gwaji akai-akai a makonnin baya-bayan nan, amma kwararru a Brazil da Indiya sun ce ba a yin gwajin sosai, don haka akwai yiwuwar da masu dauke da cutar da dama da ba a sani ba.

    Haka zalika ana duba yawan al'ummar kowace kasa. Amurka na da yawan mutane har miliyan 330, yayin da Indiya ke da biiyan 1.3. Sannan akwai kananan kasashen da suke da masu dauke da cutar da yawa duk da cewa yawan al'ummarsu bai kai na manyan kasashe biyar din can ba.

  2. An buɗe makarantu a Afrika Ta Kudu

    Ana ci gaba da buɗe makarantu a Afrika Ta Kudu bayan da gwamnatin ƙasar ta sassauta matakan kulle, inda ministan ilimi ya ce kashi 95 cikin 100 na makarantun sun cimma duk dokokin da aka sanya musu na buɗewa.

    Gwamnati ta yi feshin magani a harabar makarantu ta kuma samar da takunkumai da rigunan kariya. An ɗage komawa makarantun da mako ɗaya saboda a samu damar bin dukkan matakan da suka dace.

    Manema labarai sun yi ta rarraba bidiyo na yadda ɗalibai ke ɗaukar darasi bayan da suka koma ajujuwanzu a ranar Litinin.

    Shugabannin makarantu suna aikin tabbatar da cewa ɗalibai na bin dokokin nesa-nesa da juna da aka gindaya musu, da yawan wanke hannu da kuma gwada zafin jikinsu a yayin da suka isa makarantar.

    Minista Angie Motshekga ta ce suna aiki kan makarantun da ba su buɗe ba, inda suke fuskantar babban ƙalubalen tsaftace harabar.

    Ta kuma bayyana lalata makarantun da aka yi a lokacin da suke rufe a matsayin wani ƙalubalen.

    Ministar ta ce babu makarantar da za a bari ta buɗe idan har ba ta dauki matakan da suka kamata ba. amma babu dalibin da za a bari a baya.

  3. Mataimakin shugaban Sudan ta Kudu ya warke daga cutar korona

    Mataimakin shugaban Sudan ta Kudu Riek Machar da mai dakinsa, Ministar Tsaro Angelina Teny, sun warke daga cutar korona, a cewar kafofin watsa labaran kasar.

    Jaridar Sudan Tribune ta ambato wata sanarwa daga ofishin Mr Machar tana cewa an sallame su daga wurin killace masu dauke da cutar korona ranar Asabar "bayan sun warke sarai".

    Sanarwar ta kara da cewa an sallami mata da mijin ne bayan an sake yi musu gwaji wanda ya nuna cewa sun warke daga cutar.

    “Ana sa ran jami'an gwamnatin biyu za su koma bakin aiki nan ba da jimawa ba, watakila ranar Litinin 8 ga watan Yuni, 2020,” a cewar sanarwar.

  4. Man City da Chelsea na zawarcin Chilwell

    Manchester City ta shirya yin gogayya da Chelsea a yunkurin dauko dan wasan Leicester City mai shekara 23 dan kasar Ingila, Ben Chilwell, idan kwangilarsa ta kare, a cewar jaridarTelegraph.)

    Napoli ba za ta rage farashin dan wasan Senegal dan shekara 28 Kalidou Koulibaly daga £100m ba, duk da matsalar rashin kudin da kungiyoyi ke ciki sakamakon cutar korona. Ana rade radin dan wasan zai koma Manchester United.(Mirror)

    Manchester United da Real Madrid suna sanya ido kan halin da dan wasan Inter Milan dan kasar Argentina Lautaro Martinez, mai shekara 22, yake ciki bayan yunkurinsa na komawa Barcelona ya ci tura.(Marca via Mirror)

    Dan wasan Juventus dan kasar Bosnia-Herzegovina Miralem Pjanic, mai shekara 30, ya yi watsi da tayin da Chelsea da Paris St-Germain suka yi masa na komawa daya daga cikinsu saboda yana son komawa Barcelona.(Marca)

  5. Gwamnan Abia Okezie Ikpeazu ya kamu da cutar korona

    Gwamnan jihar Abia da ke kudu maso gabashin Najeriya, Okezie Ikpeazu, ya kamu da cutar korona.

    Wata sanarwa da Kwamishinan watsa labarai na jihar John Okiyi Kalu ya fitar ranar Litinin ta ce tuni aka killace Gwamna Ikpeazu.

    Sanarwar ta kara da cewa gwamnan ya umarci mataimakinsa ya jagoranci jihar a matsayin riko sai ranar da ya samu sauki.

    ”Za ku iya tunawa cewa ranar Asabar, 30 ga watan Mayu 2020, Gwamna Okezie Ikpeazu don radin kansa ya amince a yi masa gwajin COVID-19 kuma ya bayar da umarni a yi wa 'yan majalisar zartarwar jihar gwajin. Ranar Talata, 2 ga watan Yuni 2020 sakamakon gwajin ya nuna cewa Gwamna Ikpeazu ba ya dauke da cutar,” a cewar Kwamishinan.

    Ya kara da cewa: "Ranar 4 ga watan Yuni 2020, gwamnan ya sake mika samfur ga hukumar yaki da cutuka masu yaduwa NCDC, kuma gwajin ya nuna cewa yana dauke da cutar".

  6. Waiwaye

    Kafin mu tsunduma cikin labaran da ke faruwa yau Litinin, bari mu dan yi muku bitar abubuwan da suka wakana a karshen mako:

    • An buɗe coci-coci a Abuja ranar Lahadi
    • 'Boko Haram ta kashe sojojin Najeriya 6 a Borno'
    • Joe Biden ya fara samun goyon bayan manyan ƴan Republican
    • Korona ta sake ɓulla Sokoto da Kebbi
    • Buhari ya ce 'yan Biafra na amfani da Kiristanci don yaƙar Najeriya
  7. Barkanmu da safiya

    Nasidi Adamu Yahaya ne yake yi muku barka da wannan safiya ta Litinin, 8 ga watan Yni, 2020.

    Muna fatan ku kasance tare da mu tsawon wannan rana domin sanar da ku halin da duniya take ciki.

    Za mu kawo muku labarai da rahotannin da suka shafi rayuwarku, musamman kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da makwabtansu, har ma da sassan duniya.

    Kuna iya tafka muhawara da bayyana ra’ayoyinku a shafukanmu na sada zumunta a BBC Hausa.