Ƙarin mutum 14 sun warke daga cutar korona a Kaduna
Gwamnan Kaduna da ke Najeriya, Nasir El-Rufai, ya ce karin mutum goma sha hudu sun warke daga cutar korona a jihar.
Ya bayyana haka ne a shafinsa na Twitter ranar Alhamis da almuru.
Ya ce ko da yake an sallami mutanen da suka warke, amma an samu karin mutum 20 da suka kamu da cutar a ranar.
Mutanen da suka harbu da cutar sun fito ne daga kananan hukumomin Zaria, da Sabongari, da Chikun da Kaduna South, da Igabi, da kuma Kaduna North, in ji Gwamna El-Rufai.
Gwamnan ya kuma bukaci mazauna jIhar su ci gaba da hakurin zama a kulle, yana mai cewa taron da ya gudanar da masu rike da sarautun gargajiya na jihar ya tattauna kan yadda za a sake bude ta.
A cewarsa, kasuwanni da wuraren ibada da makamantansu za su ci gaba da kasancewa a garƙame amma a makon gobe za a dauki karin matakai kan yadda za a bude jihar sannu a hankali.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X

