An kammala jana'izar George Floyd

Wannan shafi na kawo muku bayanai kai tsaye kuma da dumi-duminsu game da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya musamman masu alaka da annobar korona da ma karin wasu daban.

Rahoto kai-tsaye

Nasidi Adamu Yahaya, Umar Mikail and Mustapha Musa Kaita

  1. Mutum hamsin 'sun mutu sakamakon korona a asibiti daya'

    Yemen

    Asalin hoton, Reuters

    Ya zuwa yanzu 'yan tawayen Houthi da ke da iko da babban birnin Yemen Sanaa basu bayyana mutane da yawa da suka kamu da cutar korona ba.

    Sai dai kaso daya cikin hudu na mutum 200 da kungiyar likitoci ta MSF take jinyarsu a Sanaa sun mutu.

    'Yan tawayen na Houthi suna boye girman barkewar cutar korona, sai dai cibiyoyi marasa yawa da ke jinyar masu cutar sun cika makil da masu fama da cutar.

    'Yan tawayen sun nemi asibitoci masu zaman kansu su taimaka musu da gadaje domin jinyar masu cutar ta korona.

    Wani likita a Sanaa - wanda ya warke daga cutar - ya ce abokan aikinsa da dama sun mutu sanadin cutar.

    Wasu rahotanni da ba a tabbatar da su ba sun ce cutar tana kama likitoci sosai, saboda rashin isassun kayayyakin kariya.

  2. Dokar kulle: El-Rufai yana taro da sarakuna

    Gwamnan jihar Kaduna da ke Najeriya, Nasir El-Rufai, yana gudanar da taro da wasu masu rike da masarautun gargajiya na jihar kan yadda za a sake bude jihar.

    A sakon da gwamna ya wallafa a shafinsa na Twitter ranar Alhamis, Gwamna El-Rufai ya ce yana "taro da Majalisar Sarakunan jihar Kaduna a matsayin wani bangare na tattaunawar da gwamnatin Kaduna take yi da masu ruwa da tsaki a kan sake bude jihar."

    Bai yi karin bayani kan taron ba, amma a makon nan Gwamna El-Rufai ya ce gwamnati bata sake bude kasuwanni da wuraren ibada ba, wadanda aka rufe a watan Maris don dakile yaduwar cutar korona.

    Ya yi kira ga mazauna jihar da shugabanni su ci gaba da hakuri sannan su bayar da hadin kai wajen aiwatar da matakan sake bude jhar.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  3. Bill Gates: Ya kamata a kai riga-kafi kowacce kasa ta duniya

    Attajirin nan dan kasar Amurka Bill Gates ya yi kira da a raba duk wani riga-kafin da aka samu na cutar korona zuwa "dukkan fadin duniya”.

    Gates yana magana ne da BBC gabanin taron da za a yi nan gaba kadan ta hanyar intanet a kan riga-kafin cutar wanda shugabannin duniya da wasu daga cikin kamfanoni masu arziki za su halarta, inda za a tara $7.4bn don samar da riga-kafin cutar.

    Ya ce taimakon da ake bukata yanzu na samar da riga-kafin cutar korona ya fi na "kowanne lokaci a baya" kuma duk wani tallafi da za a bayar zai taimaka "mana wajen ceto karin rayuka da dama".

    Za a tara kudin ne domin samar da riga-kafin cutar korona ga matalautan kasashe, yayin da kuma zai taimaka wajen yin riga-kafin wasu cututtukan masu kisa irin su shan-inna, zazzabin taifod da kuma kyanda.

    Cutar korona ta sa an dakatar da riga-kafin cututtuka a dukkan fadin duniya, kuma hakan na nufin ba a yi wa jarirai kimanin miliyan 80 riga-kafin da aka saba yi musu ba.

    Sai dai Gates ya yi gargadi kan labaran karya da ake watsawa game da riga-kafin yana mai cewa yana barazana ga yunkurin dakile yaduwar cutar korona.

    Bill Gates

    Asalin hoton, Getty Images

  4. Atiku yana so a yi wa dokokin fyade kwaskwarima

    Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar, ya yi kira ga hukumomin kasar su yi wa dokokin fyade garambawul ta yadda masu yi wa mutane fyade ba za su kubuta ba.

    "Lokaci ya yi da za mu yi kwaskwarima ga dokokin fyade domin mu tabbatar masu yin sa basu zille wa bincike, da gurfanarwa a gaban shari'a da kuma samunsu da laifi sannan a yi hukuncin da ya dace a kansu saboda aikata wannan mummunan laifi ba," a cewar Atiku Abubakar.

    Ya bayyana haka ne a sakon da ya wallafa a shafinsa na Twitter domin nuna bakin cikinsa game da kisan da aka yi wa wata ɗaliba ƴar jami'a, Vera Uwaila, bayan wasu mutane sun yi mata fyade a jihar Edo da ke kudancin Najeriya.

    Tsohon mataimakin shugaban kasar ya ce ya yi magana da iyayenta game da batun inda "na mika ta'aziyyata a kan fyaden da kuma kisanta. Abin bakin ciki shi ne yadda fyade ya zama ruwan dare a kasar nan".

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  5. 'An yi wa mata 100 fyade a Ethiopia' lokacin dokar kulle

    Ethiopia

    Asalin hoton, Getty Images

    Hukumomi a Ethiopia sun ce 'yan mata fiye da 100 aka yi wa fyade sannan aka kai su asibiti a babban birnin kasar, Addis Ababa, tun da cutar korona ta barke a kasar, a cewar gidan talbijin mai zaman kansa Walta TV.

    Shugabar ofishin kula da harkokin mata da yara a Addis Ababa, Almaz Abraham, ta ce ana samun karin matsalar cin zarafin mata saboda an rufe makarantu sakamakon yaduwar cutar korona.

    "An yi wa kananan yara mata dari da daya fyade a wata biyu da suka wuce bayan barkewar annobar Covid-19. Matsalar ita ce, ba kamar lokacin da makarantu suke a bude ba, ba a gane an yi wa yarinya fyade yanzu sai ta dauki ciki. Watakila akwai damar hana ci gaban wannan matsala idan aka koma makaranta," a cewarta.

    Ta kara da cewa: "Mazan da suka saba yi wa mata fyade a waje yanzu suna yi wa 'ya'yansu fyade a gidajensu."

  6. Cutar korona ta kashe 'yan majalisar Pakistan

    'Yan majalisar dokokin Pakistan biyu sun mutu sakamakon Covid-19 ranar Laraba a yayin da kasar ta bayar da sanarwar samun kari mafi girma na mutanen da suka kamu da cutar inda sabbin mutum 4,772 suka harbu da ita, a cewar jaridar Dawn.

    Daga bisani a ranar ta Laraba, wani dan majalisa daga lardin Punjab, Shaukat Manzoor Cheema, ya mutu sakamakon kamuwa da cutar korna, in ji jaridar.

    A farkon makon nan, Firaministan Imran Khan ya kare matakin da ya dauka na sassauta dokar kulle, yana mai cewa tana kawo tabarbarewar tattalin arziki don haka babu yadda za a yi illa kawai mutane su san yadda za su "gudanar da rayuwa tare da cutar".

    Mutum 83,000 aka tabbatar sun harbu da cutar korona a Pakistan inda mutum 1,688 suka mutu.

  7. Wanne tsegumi ake yi a fagen wasannin kwallon kafa?

    Real Madrid tana son dauko dan wasan Borussia Dortmund dan shekara 20 Jadon Sancho.(AS)

    Juventus ta tuntubi Barcelona da zummar karbo aron dan wasan Faransa Ousmane Dembele, mai shekara 23, a bazara.(Mundo Deportivo - in Spanish)

    Fatan kocin Manchester United Ole Gunnar Solskjaer na kara nauyin aljihun kungiyar ta hanyar sayar da dan wasan Argentina Marcos Rojo, mai shekara 30, da Chris Smalling da kuma dan wasan Chile Alexis Sanchez, mai shekara 31, zai gamu da cikas saboda rashin kudin da kungiyoyi suke fama da shi sakamakon cutar korona.(Evening Standard)

    Dan wasan Bournemouth Ryan Fraser, mai shekara 26, wanda ya shirya barin kungiyar don zaman aro, yana iya zama daya daga cikin 'yan wasan da kungiyoyi suka fi bukata a gasar Premier.(The Athletic - subscription only).

    Jadon Sancho

    Asalin hoton, Getty Images

    Bayanan hoto, Jadon Sancho
  8. Matsalar fyade tana dugunzuma ni – Aisha Buhari

    Aisha Buhari, mai dakin shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ta ce labarin da take samu game da yawaitar yi wa mata fyade yana matukar tayar mata da hankali.

    A sakon da ta wallafa ranar Laraba a shafinta na Twitter, Aisha Buhari ta ce: "Abin tayar da hankali ne samun labarin kisan da ake yi wa 'ya'yanmu mata, wadanda maza suke yi wa fyade na rashin imani; wasu lokutan ma iyayensu da 'yan uwansu da kuma masu kula da su ne suke yin hakan."

    Matsalar fyade dai tana neman zama ruwan dare a Najeriya, inda a baya bayan nan aka samun labarin yi wa wasu mata fyade a sassa daban-daban na kasar.

    Daya daga cikinsu ita ce wata yarinya mai shekara 12 wacce ta shaida wa 'yan sanda a jihar Jigawa da ke arewa maso yammacin kasar cewa wasu mutum 12 sun shafe wata biyu suna yi mata fyade.

    Kazalika, a makon jiya an zargi wasu mutane da kisan wata ɗaliba ƴar jami'a bayan sun yi mata fyade a jihar Edo da ke kudancin Najeriya.

    Masu rajin kare hakkin yara a Najeriya na ganin cewa za a ci gaba da fuskantar matsalar fyade ga kananan yara a kasar matukar gwamnati ba ta fara aiwatar da hukuncin kisa a kan masu aikata irin wannan laifi ba.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  9. Barkanmu da safiya

    Daga na Sashen Haus na BBC muke yi muku barka da wannan saiya ta Alhamis.

    Muna fatan ku kasance tare da mu tsawon wannan rana domin sanin halin da duniya take ciki.

    Za mu kawo muku labarai da rahotannin da suka shafi rayuwarku, musamman kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da makwabtansu, har ma da sassan duniya.

    Kada ku manta kuna iya tafka muhawara da bayyana ra'ayoyinku a shafukanmu na sada zumunta a BBC Hausa.