Covid-19: An sallami ƙarin almajirai 44 a Gombe

Wannan shafi na kawo muku bayanai kai tsaye kuma da dumi-duminsu game da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya musamman masu alaka da annobar korona da ma karin wasu daban.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail and Nasidi Adamu Yahaya

  1. Sojoji sun kashe ‘yan bindiga 200 a Katsina da Zamfara

    Jirgin sojan Najeriya

    Asalin hoton, Others

    Dakarun rundunar Hadarin Daji karkashin sojojin sama na Najeriya sun hallaka kusan 'yan bindiga 200 a jihohin Katsina da Zamfara.

    Sojojin sun hallaka su ne a wani hari da suka kai ta sama a sansanonin ɓarayin da ke Mai'Bai a ƙaramar hukumar Jibiya a jihar Katsina da kuma sansanin Kurmin Kura a ƙaramar hukumar Zurmi ta jihar Zamfara a ranakun Juma'a da Asabar.

    A wata sanarwa da Shelkwatar Tsaro ta Najeriya ta wallafa a shafinta na Twiitter, ta bayyana cewa an ƙaddamar da harin ne bayan an ɗauki lokaci ana tattara bayanan sirri inda aka gano ɓarayin na amfani da wuraren biyu a matsayin maɓuyarsu.

  2. Ƙarin mutum 289 sun kamu da korona, 10 sun mutu a Jamus

    Jamus

    Asalin hoton, Getty Images

    Jamus ta bayar da rahoton ƙarin mutum 289 da suka harbu da cutar korona da kuma 10 da suka rasa rayukansu.

    Alƙaluman na Litinin kan yi ƙasa saboda tsaikon da ake samu na fitar da rahoto a ranakun ƙarshen mako.

    Sai dai tun bayan sassauta dokokin kulle a Jamus, ba a samu hauhawar yawan masu kamuwa da cutar ba ko kuma mutuwa, amma an tilasta wa mutane saka takunkumi.

    Kashi 52% na jumillar waɗanda suka kamun mata ne, 48% kuma maza. Kashi 2% kacal ne na yara 'yan ƙasa da shekara 10.

    Yunƙurin yi wa kowa da kowa gwaji a Jamus na nufin waɗanda suka nuna ƙananan alamun cutar da waɗanda ma ba su nuna ba ana saka su cikin alƙaluman.

    Jami'ar Johns Hopkins ta ce mutum 180,328 ne suka kamu jumilla a Jamus, sai kuma 8,287 da suka rasu.

  3. Ko sauyin yanayi ya haifar da zafi mai kisa?

    Wani mutum na shan ruwa

    Asalin hoton, Getty Images

    Masu bincike a bangaren sauyin yanayi sun dade suna gargadin cewa doron kasa zai fuskanci yanayi wanda "kusan mutane ba za su iya zama a kansa ba" zuwa shekarar 2070.

    Amma wani sabon bincike da aka wallafa a mujallar kimiyya ta Science Advances ya gano cewa an fara fuskantar wannan yanayi.

    Yanayi masu hadari da suka hada zafi da rashin kadawar iska na bayyana a fadin duniya, kuma duk da cewa wadannan yanayi kan faru ne tsawon sa'o'I, suna faruwa a-kai-a-kai kuma suna da tsanani, a cewar masu binciken.

  4. Za a sassauta dokar kulle a Afirka ta Kudu

    Cyril Ramaphosa

    Asalin hoton, Getty Images

    Shugaban Afrika ta kudu Cyril Ramaphosa ya sanar da cewa ƙasar za ta soma sassauta dokar hana fita a cikin makonni masu zuwa, duk da cewa masu kamuwa da cutar korona na ƙaruwa.

    Akwai mutane da dama da za a bai wa damar komawa bakin aiki, za kuma a ɗage dokar hana fita kwata-kwata, sannan za a riƙa sayar da barasa domin sha a gidaje.

    A jawabin da ya gabatar ga 'yan ƙasar, Mista Ramaphosa ya ce dokar kulle ta taimaka wajen taƙaita cikowa a asibitoci -- sai dai ya yi gargaɗi cewa cutar na iya sake yaɗuwa sama da abin da ake gani a yanzu kafin ta sassauta.

  5. Barkanmu da safiyar Tushen Aiki

    Masu bibiyarmu barkanku da safiyar Litinin - Tushen Aiki - wadda ta yi daidai da ɗaya ga Sallah Ƙarama.

    Umar Mikail ke fatan an tashi lafiya a shafinmu na labarai kai-tsaye kan halin da duniya ke ciki musamman game da annobar cutar korona.

    Ai se mu shiga abin da ya kawo mu kawai.