Eid-al-Fitr: El-Rufai ya jinjina wa Musulmi kan dokar kulle

Wannan shafi na kawo muku bayanai kai tsaye kuma da dumi-duminsu game da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya musamman masu alaka da annobar korona da ma karin wasu daban.

Rahoto kai-tsaye

Umar Mikail and Mustapha Musa Kaita

  1. Muna sake yi muku barka da sallah

    BBC
  2. Abin da ya kamata ku sani game da saka takunkumi

    Bayanan bidiyo, Latsa hoton da ke sama ku kalli yadda ake saka takunkumin
  3. Korona: Ba wanda ya kamu, ba wanda ya mutu, ba wanda ya warke a Kano ranar Asabar

    Ma'aikatar Lafiya ta Jihar Kano ta ce ba a samu wani ƙarin mutum da ya kamu ko ya warke ko ya mutu ba sakamakon cutar korona a jihar ranar Asabar.

    Alƙaluman da maikatar lafiyar ta wallafa sun nuna cewa har yanzu waɗanda suka kamu da cutar suna nan a 883 kamar yadda suke a ranar Juma'a.

    "Kano ba ta samu wanda ya kamu ba, babu wanda aka sallama sannan babu wanda ya mutu," in ji ma'aikatar, a wani saƙon Tiwtter.

    Ya zuwa ƙarfe 11:50 na daren Asabar, 23 ga watan Mayu, mutum 883 ne suka kamu jumilla, sai 36 da suka rasu, an sallami 133 da kuma 714 da ke jinyar cutar a yanzu.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  4. Mutum fiye da dubu 100 sun harbu da korona a Afirka

    Afirka

    Asalin hoton, Getty Images

    Alƙaluman da hukumar da ke yaƙi da cutuka masu yaɗuwa a Afirka, CDC Africa, ta fitar sun nuna cewa mutum fiye da dubu 100 ne suka harbu da cutar korona a ƙasashe 54 mambobin Ƙungiyar Haɗin Kan Afirka ta AU.

    CDC ta ce mutum 107,412 ne suka harbu ya zuwa ƙarfe 9:00 na safiyar Lahadi, 24 ga watan Mayu.

    Kazalika, hukumar ta ce mutum 3,246 sun mutu, yayin da 42,626 suka warke daga cutar.

    Kauce wa X
    Ya kamata a bar bayanan X?

    Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.

    Gargadi: BBC ba za ta dauki alhakin bayanan da aka wallafa a shafukan da ba nata ne ba.

    Karshen labarin da aka sa a X

  5. Barka da Sallah

    Barkanmu da Idin Ƙaramar Sallah tare da fatan Allah ya maimaita mana.

    Umar Mikail ke muku maraba da shigowa shafinmu na labarai kai-tsaye - kuna cin tuwon sallah kuna ganin yadda duniya ke ciki.

    Ku biyo mu kawai.