Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Ba za mu lamunci tashin farashin kayayyaki ba – Ganduje

Wannan shafi yana kawo muku bayanai kai tsaye dangane da annobar korona da ke ci gaba da yi wa duniya fyadar 'ya'yan kadanya.

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir and Umar Mikail

  1. Coronavirus: Fursunoni sun kona gidan yari a Sierra Leone

    Fursunoni a Sierra Leone sun yi yunkurin ballewa daga gidan yari sakamakon wasu da suke zargin na da cutar korona da aka kai jarun din.

    An kashe mai tsaron fursunonin guda daya yayin hatsaniyar inda kuma mutane da dama suka samu raunuka a gidan yarin da ke kan titin Pandemba Road a birnin Freetown. An dai kone gidan yarin.

    Gidan yarin Pandemba Road na cin mutum 300 bisa ka'ida amma yanzu haka yana da fursunoni 1,000.

    An dakatar da yanke hukunce-hukunce tun bayan rufe kotuna sakamakon matakin hana bazuwar cutar korona da kasar da dauka.

    Yanzu haka dai Sierra Leone 104 sannan mutum hudu sun mutu..

  2. Cutar korona ta kashe mutum biyu a Yemen

    Cutar korona ta kashe mutum biyu a karon farko a Yemen, abin da ya janyo tsoron barkewar annobar da kan iya jefa kasar da yaki ya daidaita cikin wani sabon tashin hankalin.

    Mutum biyun dai wadanda suka mutu a asibitin kudancin birnin Aden 'yan uwane, inda tun da farko gwamnati ta ce akwai mutum biyar da suka kamu da cutar a yankin.

    Shekaru biyar da aka kwashe ana yaki a Yemen ya lalata tsarin kiwon lafiyar kasar, wanda ya bar kasar cikin damuwar yadda za ta shawo kan wannan annoba.

    Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadin cewa, cutar za ta iya bazuwa a kasar matukar ba a dauki matakan gudanar da bincike ba a kan lokaci.

  3. Mun dade ba mu ji duriyar Kim Jong-un ba - Pompeo

    Sakataren harkokin Amurka, Mike Pompeo ya ce jami'an Amurka sun ce ba su ga shugaban Koriya ta Arewa ba a 'yan kwanakin nan, Kim Jong-un kuma suna sa ido kan rahotannin lafiyarsa.

    Ya kuma bayyana damuwarsa dangane da hasashen da suke da shi na barkewar annobar korona ko kuma yunwa.

    Mista Kim mai shekara 36 dai ba a kara ganin sa a bainar jama'a ba tun ranar 12 ga watan Afrilu lokacin da ya bayyana a gidan talbijin din kasar.

    To sai dai jami'an gwamnatin Koriya ta Kudu sun ce rahotannin ba gaskiya ba ne.

    Rashin bayyanar Kim Jong-un a wasu tarukka da ya saba halarta ne dai ya janyo rade-radin ko shugaban na Koriya ta Arewa na raye cikin koshin lafiya.

  4. China na kokarin kayar da ni a zaben Nuwamba - Trump

    Shugaban Amurka, Donald Trump ya ce kasar China "za ta yi duk mai yiwuwa" wajen ganin bai sake cin zabe ba a karo na biyu.

    Mista Trump ya fadi haka ne yayin wata hira da kamfanin dillancin labarai na Reuters a fadar White House, inda ya ce China na fuskantar wasu abubuwa daga Amurka sakamakon barkewar cutar korona.

    Ya ce ya kamata China ta kyale duniya ta san hakikanin abin da ke faruwa dangane da wannan cuta mai yaduwa.

    Donald Trump ya ce China na kokarin ganin abokin hamayyarsa na jam'iyyar Dimokrat, Joe Biden ya buge shi a zaben watan Nuwamba.

    Mista Trump ya kara da cewa yana shakkar alkaluman da ke nuna Mista Biden zai lashe zaben watan na Nuwamba.

  5. Labarai da dumi-dumi, 'Almajirai daga Kano 19 ne suka sa yawan masu korona ya karu a Kaduna'

    Gwamnan Jihar Kaduna Nasir Elrufa'i ya ce sun samu karin mutum 19 masu dauke da cutar korona, al'amarin da ya kara yawan adadin masu cutar a jihar daga 9 zuwa 25.

    Elrufa'i wanda ya wallafa wannan bayani a shafinsa na Twitter, ya ce an yi wa almajirai 40 gwaji, inda sakamakon 19 daga cikinsu ya nuna suna dauke da cutar ta korona.

    Gwamna Elrufa'i ya kuma kara da cewa yanzu ta tabbata shige da fice da ake yi wa jihar tasa ne ke janyo karuwa masu cutar a Kaduna, inda ya ja hankalin jami'an tsaro da su ci gaba da sanya ido kan duk masu shiga birnin ta barauniyar hanya.

    Ko a makon da ya gabata ma sai da gwamnan ya sanar cewa sun samu biyar daga cikin almajiran da aka mayar wa jihar tasa daga Kano masu dauke da cutar.

    Kokarin dakile bazuwar cutar korona a birnin Kano ne dai ya sa Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya fito da shirin mayar da almajirai jihohinsu na asali.

    Masana harkar lafiya da dama sun soki shirin bisa dogaro da cewa hakan ka iya fantsama cutar a wasu jihohin da ba su da ita.

  6. Coronavirus: 'Yan Tunisia za su shiga kulle

    Gwamnatin Tunisia ta sanar da shirinta na fara sassauta dokar hana zirga-zirga daga ranar Litinin mai zuwa.

    'Yan kasar dai sun fuskanci mawuyacin halin rayuwa saboda matakai masu tsanani da hukumomi suka dauka domin yaki da cutar korona.

    Kawo yanzu kasar na da kusan mutum 1,000 da suka kamu da cutar, kuma 40 cikinsu sun mutu.

    Yankin arewacin Afirka dai na da masu dauke da cutar korona da dama.

  7. Coronavirus: Pompeo ya caccaki Afirka ta Kudu kan karbar likitocin Cuba

    Sakataren harkokin wajen Amurka, Mike Pompeo ya caccaki kasar Afirka ta Kudu bisa karbar likitocin kasar Cuba fiye da 200 da za su taimaka wa kasar yakar annobar korona.

    Mista Pompeo ya zargi Cuba da kokarin amfana daga annobar korona kamar yadda kamfanin dillancin Labarai na AFP ya rawaito.

    "Mun fahimci gwamnatin Cuba na cin gajiyar wannan annoba ta hanyar zaluntar ma'aikatan lafiyarta."

    A ranar Lahadi ne dai tawagar ma'aikatan lafiyar ta kasar ta Cuba da ta kunshi likitoci da kwararru kan annoba da sauran su ta sauka a Afirka ta Kudu, inda za a rarraba su zuwa lungu da sakon kasar.

    Shigar tawagar ma'aikatan lafiyar ta Cuba Afirka ta Kudu dai na samun suka daga bangarori daban-daban, inda kungiyar likitocin kasar ita ma ta soki al'amarin.

    Afirka ta Kudu dai na da masu dauke da cutar korona 5,350, inda mutum 103 suka mutu.

  8. Firai Ministan Guinea Bissau ya kamu da cutar korona

    Firai MInistan kasar Guinea Bissau, Nuno Gomes Nabiam ya kamu da cutar korona, kamar yadda ma'aikatar lafiyar kasar ta sanar.

    Ministan cikin gida, Botche Cande da karin wasu ministocin guda biyu su ma na dauke da cutar ta Covid-19.

    Mista Nabiam ya ce da dama 'yan kwamitin ministoci kan annobar korona a kasar na dauke da cutar.

    Guinea Bissau ta tabbatar da samun masu cutar 205 inda mutum daya ya mutu.

  9. Batun sanya takunkumi saboda korona na tayar da kura a Legas

    'Yan Najeriya mazauna Legas na ci gaba da mayar da martani kan umarnin gwamnatin jihar cewa nan gaba dole ne kowa ya sa takunkumi.

    Matakin dai na zuwa ne a makon karshe na dokar kulle da gwamnatin tarayya ta sanya a kan jihar da sauran wurare.

    Da dama 'yan jihar na fadin cewa takunkumin na rike musu numfashi saboda haka ba sa maraba da yin amfani da shi.

    Jihar Legas dai ce a gaba wajen yawan masu dauke da cutar korona a Najeriya, inda take da adadin mutum 931.

  10. Masu korona a Najeriya sun kai 1728

    Hukumar dakile cutuka masu yaduwa a Najeriya, NCDC, ta ce mutum bakwai ne suka rasu a jiya Laraba sakamakon cutar korona a kasar.

    Sabbin alkaluman da ta fitar a daren jiya na cewa mutum 196 sun sake kamuwa, inda yanzu haka yawan masu cutar a Najeriya ya karu zuwa 1,728.

    A karon farko, an samu bullar korona a jihar Yobe, inda NCDC ta ce mutum daya ya kamu, yanzu dai Kogi da Cross river ne kawai a Najeriya annobar ba ta kai gare su ba.

    Haka zalika, fiye da mutum 100 ne cutar ta harba a arewacin Najeriya cikin kwana daya kamar yadda alkaluman NCDC suka nuna.

    To sai dai hukumar ta ce masu cutar 52 ne suka warke a jiya Laraba, adadi mafi yawa da aka taba samu tun bayan bullar korona a kasar.

    Yanzu haka adadin wadanda suka warke a kasar ya kai 307.

  11. Kungiyar agaji ta Save the Children ta yi gargadin cewa yankin kusurwar Afirka na fuskantar barazana uku da ba a taba ganin irinta ba, lokacin da annobar korona ta auka wa yankin mai fama da farin dango, ga kuma ambaliyar ruwa.

    Kungiyar ta ce kananan yara sama da miliyan biyar ne tuni ke fama da matsanancin karancin abinci mai gina jiki ga kuma annobar korona a yanzu ta shafi tattalin arziki da harkokin kula da lafiyar al'ummar yanki.

    Ana fargabar samun karuwar farin dango masu cinye amfanin gona yayin da koguna suka tumbatsa sakamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya.

    Miliyoyin fari ne ke zuba kwayaye, kuma ana sa ran sabbin kyankyasar za su sake mamayar gonaki a watan Yuni.

    Kungiyar Save the Children ta bukaci kasashen duniya su agaza wa Somaliya da Kenya da Habasha cikin gaggawa, domin a cewarta lamarin ya fi karfinsu.

  12. Fadar White House ta yaba da gwajin maganin kashe cututtuka

    Jagoran mashawarta kan fannin lafiya a fadar White House ya yaba wa sakamakon gwajin wani maganin kashe kwayar cuta da ya ce ya rage lokacin da masu cutar korona ke shafewa a gadon asibiti kafin su warke.

    Dr. Anthony Fauci ya ce bayanai sun nuna cewa maganin Remdesivir na da wani fayyataccen tasiri kan wannan cuta.

    Hukumar Lafiya ta Duniya ta ja bakinta ta tsuke kan batun. Dr Mark Ryan, daga Hukumar Lafiya ya ce a wani lokaci tana iya daukar bayanan da aka wallafa don tabbatar da sahihancin maganin.

    Ba a dai wallafa bayanai kan gwajin ko yin bitarsu daga wasu masanan kimiyya masu zaman kansu ba, abin da ke nufin ba za a hakkake kan sahihancin maganin ko amfaninsa ba.

    A makon jiya Hukumar Lafiya ta yi azarbab'in wallafa bayanai kan wani gwajin wannan magani na Remdesivir a China da ke nuna samun kankanuwar nasara.

  13. Ba a sake samun mai cutar korona a Korea ta Kudu ba

    Tun bayan barkewar annobar korona sama da wata biyu a Koriya ta Kudu, a karon farko ba a samu ko mutum daya a cikin gida da ya kamu da cutar ba.

    Mutum hudu sabbin kamu da aka tabbatar a ranar Alhamis, dukkaninsu sun shiga kasar ne daga ketare.

    Adadin masu kamuwa da cutar ya ragu tsawon makwanni bayan kasar wadda ta kasance daya daga cikin kasashen da cutar ta fi muni ta yi kokarin shawo kanta ta hanyar wani gwaji na musamman da bin sawun mutanen da suka yi hulda da masu cutar.

    Kasar Japan ce dai mai shirin karbar baki a gasar Olympics ta 2020 da ake sa ran yi idan cutar korona ta bari.

  14. Coronavirus: Ba zan tsawaita matakan tazara tsakanin jama'a ba - Trump

    Shugaba Donald Trump ya ce ba zai tsawaita matakan samar da tazara tsakanin jama'a ba, a daidai lokacin da mace-macen da annobar korona ta haddasa a Amurka suka zarce mutum dubu sittin.

    Matakan wadanda wa'adinsu ke karewa ranar Alhamis na karfafa gwiwar Amurkawa su yi aiki daga gida kuma su guji shiga manyan taruka.

    Maimakon haka, Mista Trump ya nanata muhimmancin bunkasa tattalin arziki, wanda ya durkushe da kashi biyar cikin 100 a watannin ukun farko na wannan shekara.

    Jerome Powell, jami'i a baitulmalin kasar ya ce Amurka na fuskantar wani lokaci na koma-bayan tattalin arziki mafi muni a tarihinta saboda tarnakin da aka sa don annobar korona.

  15. Farawa

    Masu bibiyarmu barkan ku da warhaka. Da fatan kuna cikin koshin lafiya. Za mu ci gaba da kawo muku bayanai kai tsaye dangane da annobar korona a sassan duniya. Da fatan za ku kasance da shafin bbchausa.com. Mun gode.