Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Tambuwal ya hana mahaifin Rahamaniyya shiga Sokoto

Wannan shafin na kawo muku abubuwan da ke faruwa a duniya baki daya dangane da annobar coronavirus.

Rahoto kai-tsaye

Usman Minjibir, Awwal Ahmad Janyau, Umar Mikail and Buhari Muhammad Fagge

  1. Adadin masu cutar korona a Sipaniya ya yi kasa

    Adadin wadanda ke mutuwa saboda cutar korona a Spaniya ya yi kasa da dari hudu, a karon farko tun bayan da Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana ta a matsayin annoba a ranar 11 ga watan Maris.

    Wannan dai ita ce rana ta biyu da adadin ke ci gaba da raguwa a jere, bayan da yawan wadanda suka mutu a kasar ya zarta 20,000 tun bayan barkewar cutar.

    Da yake jawabi ga taron manema labarai, babban jami'in lafiya na Spaniya Fernando Simon, ya ce alkalumman sun kara musu kwarin guiwa.

    Ya ce "yau a karon farko cikin lokaci mai tsawo, an samu mutane 399 da suka mutu, wadannan alkalumma sun ba mu kwarin guiwa, duk da yake ba abu ne mai dadi kulluyaumin a rika zancen wadanda suka mutu ba."

    A gefe guda babban bankin Spaniya ya ce tattalin arzikin kasar ya yi kasa da kaso biyar a watanni hudu na farkon wannan shekara.

  2. Coronavirus: An bai wa mutane damar komawa aiki a India

    Hukumomi a India sun bai wa miliyoyin 'yan kasar damar komawa aiki daga yau litinin, bayan da sabbin dokokin gwamnatin kasar suka bai wa jihohi damar saukaka dokokin hana zirga-zirga da aka kafa.

    A wasu jihohin manoma za su koma gona, saboda fargabar karancin abinci.

    Haka nan leburori da dama da ke gudanar da wasu aikace-aikacen gwamnati da suka hada da gyaran hanyoyi za su koma bakin aiki.

    BBC ta rawaito cewa lokaci ne mai muhimmanci ga kasar, yayin da aka samu adadi mafi yawa na mutanen da suka rasa rayukansu a rana guda, sun kai mutum 1,953, sai dai abu ne da zai dauki lokaci, domin kasa ce mai mutane biliyan daya da doriya.

  3. Wurin da Sheikh Ahmed Gumi zai gudanar da Tafsiri

    Fitaccen malamin addinin musuluncin nan da ke Kaduna, Sheikh Ahmed Gumi ya ce tuni ya kammala shirin fara Tafsirin Al-Qur'ani mai girma.

    Sheikh Gumi ya ce zai gudanar da Tafsirin a gidan nasa ne inda mutum 10 ne kawai za su halarta.

    Sai dai ya ce za a nadi sauti da bidiyo na karatun nasa inda daga baya za a watsa a kafafen sada zumunta.

  4. Coronavirus: Ana zanga-zanga kan dokar hana zirga-zirga a Nijer

    Matasan birnin Yamai na jamhuriyar Nijar na gudanar da zanga-zanga a lokacin da dokar takaita zirga-zirga ke aiki daga 7 na yamma zuwa 6 na safe.

    Ko a daren ranar Lahadi sai da matasan suka babaka wa unguwanni guda bakwai wuta, al'amarin da ya janyo jami'an tsaro suka yi ta harba tiyagas cikin unguwannin.

    Duk da dokar hana zirga-zirga da aka sanya, matasan na ci gaba da hawa tituna tare da kona tayoyi da farfasa ababan more rayuwa.

    A wasu wuraren ma, matasan masu zanga-zanga na far wa dukiyoyin jama'a.

    Iyaye da hukumomi da ma kungiyoyi masu zaman kansu sun yi tir da wannan lamari inda kuma suke ci gaba da yin kira ga matasan da su yi biyayya ga dokar da gwamnati ta sa da manufar takaita yaduwar cutar korona.

  5. Hare-haren sama sun kashe 'yan Boko Haram

    An kashe jagororin kungiyar Boko Haram a jihar Bornon Najeriya, kamar yadda jaridar Vanguard ta rawaito a shafinta na intanet.

    " An kashe jagororin da dama a wasu jerin hare-haren sama da rundunar Lafiya Dole da ke yaki da 'yan Boko Haram a Durbada da ke jihar Borno a arewa maso gabashin Najeriya."

    Mai magana da yawun rundunar, Manjo Janar John Enenche, a wata sanarwa ranar Litinin, ya kara da cewa an rugurguza gine-ginen 'yan ta'addar.

    Manjo Janar Enenche ya kara da cewa an kaddamar da hare-haren ne ranar 17 ga watan Afrilu.

    Rundunar sojin Najeriya dai ta dukufa wajen yaki da 'yan Boko Haram a yankin arewa maso gabashin kasar.

    A ranar 18 ga watan Afrilu an kashe fiye da 'yan Boko Haram 100 a jihar Yobe a baya-bayan nan.

    Kafafen yada labarai na Najeriya sun rawaito cewa shugaba Boko Haram, Abubakar Shekau 'na ta bin wasu mutane da manufar yi wa gwamnati magana a ba shi damar ajiye makamai."

  6. An tsawaita dokar kulle a Zimbabwe saboda cutar korona

    Shugaban Zimbabwe, Emmerson Mnangagwa ya sanr da tsawaita dokar kulle da manufar takaita yaduwar cutar korona a fadin kasar.

    To sai dai dokar ba ta shafi kafanonin kere-kere ba saboda ka da tattalin arzikin kasar ya samu tawaya.

    A ranar Lahadi ne dai ya kamata dokar ta kulle ta kare.

    Kwatsam sai shugaban ya yi wani jawabi a gidan talbijin na kasar inda ya sanar da tsawaitawar.

    Ya ce babu makawa sai an kara idan dai har ana son a dakile yaduwar cutar.

    Zimbabwe dai na da mutum 25 da masu dauke da cutar ta korona, inda uku daga cikin suka mutu sakamakon cutar.

  7. Korona ta kashe ma’aikacin agaji na MSF

    Kungiyar Likitoci ta kasa da kasa, MSF da ke aikin ceto a jihar Bornon Najeriya, ta sanar da mutuwar daya daga cikin ma'aikatanta wanda ta ce sakamakon gwaji ya nuna yana dauke da cutar korona.

    Sai dai kungiyar ba ta bayyana sunan ma'aikacin nata ba ko kuma jinsi saboda kariya.

    Wannan ne karon farko da wani ma'aikacin kungiyar agaji ya mutu sakamakon cutar korona a Najeriya.

  8. Coronavirus: Mutum 5000 sun mutu a kankanin lokaci a Equador

    A yankin Guayas, jihar da annobar korona ta fi shafa a Ecuador, lokacin da aka sake tantance alkaluman yawan mutanen da suka mutu, an fahimci wani abu.

    Mutum 6,700 sun mutu a makonni biyu na watan Afrilu, Karin mutum 5,000 fiye da yadda aka saba gani duk wata - inda wannan ya sa Guayas ya zama yankin da annobar ta fi yi wa mummunan tasiri a kasar da ma Latin Amurka gaba daya.

    Kuma mace-macen ba duka ne na Covid-19 ba: yayin da cibiyoyin lafiya suka durkushe saboda annobar, marasa lafiya da yawa da ke fama da wasu cutukan sun kasa samun kulawar da suke matukar bukata cikin gaggawa.

  9. 'Yar shekara 68 ta haifi 'yan biyu a Lagos

    Yayin da jama'a ke zaman zulumi a Najeriya sakamakon cutar korona, asibitin koyarwa na jami'ar jihar Legas ya sanar da cewa sun samu nasarar karbar haihuwar wata dattijuwa mai shekara 68 da ta haifi 'yan biyu a birnin Legas.

    Shugaban Mjalaisar Tuntuba na asibiti, Farfesa Wasi'u Adeyemo ne ya bayar da sanarwar ranar Lahadi a shafin asibitin na Twitter.

    Ya ce an yi wa dattijuwar tiyata ne a lokacin da cikin yake wata 37.

    Sanarwar ta kara da cewa uwar da danta na cikin koshin lafiya.

  10. An yi wa Abba kyari sadakar uku da ta bakwai a Borno

    Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya halarci taron addu'ar uku ta marigayi Abba Kyari.

    Iyalan marigayi Abba Kyari dai sun hade ranakun addu'ar uku da bakwai a rana daya domin gudun cunkosan jama'a.

    A ranar Juma'ar da ta gabata ne dai Malam Abba Kyari ya rasu bayan fama da cutar korona ta kimanin makonni hudu.

  11. Riga-kafi ya fi magani

  12. Adadin masu cutar korona ya kai 627 a Najeriya

    Hukumar dakile cutuka masu yaduwa a Najeriya NCDC ta tabbatar cewa zuwa yanzu mutum 627 suka harbu da cutar korona a kasar.

    Hakan na zuwa ne bayan da a ranar Lahadi da daddare NCDC ta sake sanar samun karin mutum 86 da suka kamu da cutar ranar Litinin 20 ga watan Afrilu a kasar.

    A shafinta na Tiwita, hukumar ta NCDC ta bayyana cewa a yanzu cutar Korona ta yadu a jihohin kasar 21 har da babban birnin Abuja.

    Daga cikin na bayan nan da ta sanar, 70 daga cikinsu sun fito ne daga Legas sai bakwai a Abuja da uku a Katsina da wasu karin uku a Akwa Ibom sai mutum 1 a Jigawa da 1 Bauchi da kuma karin wani a Borno.

    Karon farko ke nan da aka samu bullar wannan annoba a jihohin Jigawa da Borno.

    Ana jin wadannan ne alkaluma mafi yawa na mutanen da suka kamu da cutar korona rana daya a Najeriya da hukumar ta fitar tun bayan fara samun annobar ranar Alhamis 27 ga watan Fabrairu.

  13. Coronavirus: Alkaluman masu cutar na karuwa a Spaniya

    Alkaluman mutanen da ke duake da cutar korona a kasar Spaniya sun karu zuwa 200,210 in ji ma'aikatar Lafiya ta kasar.

    Kimanin mutum 400 ne suka mutu a ranar Lahadi inda adadin wadanda suka mutu ya zama 20,852.

    Spaniya ce ta biyu a kasashen duniya masu yawan mutanen da ke dauke da cutar korona, bayan Amurka, in ji jami'ar Johns Hopkins University.

  14. Coronavirus: Halin da ake ciki a Burtaniya

    • Mutum 16,060 ne suka mutu a fadin Burtaniya, kamar yadda alkaluman gwamnatin Burtaniya suka nuna.
    • Mutum 14,400 ne suka mutu sakamakon cutar a yankin Ingila.
    • Mutum 575 ne suka mutu a yankin Wales.
    • Mutum 194 sun mutu a Arewacin Ireland
    • A Scotland, mutum 903 suka mutu
    • Daga cikin mutum 372,967 da aka yi wa gwajin cutar korona, mutum 120,067 suke dauke da cutar.
  15. Coronavirus: Ghana ta janye dokar hana zirga-zirga

    Shugaban Ghana Nana Akufo-Addo ya janye matakin hana zirga-zirga da ya sanya a wasu yankunan kasar Ghana, inda ya bukaci 'yan kasar su rufe fuskokinsu da takumkumi.

    Shugaban ya janye dokar a Accra, babban birnin kasar da Kumasi birni na biyu mafi girma da kuma Tema .

    Biranen sun kasance cikin dokar hana fita tsawon mako uku don kare yaduwar annobar korona.

    Kasar a yanzu ta tabbatar da samun fiye da mutum 1000 masu cutar, tara daga ciki sun rasu.

  16. Covid-19: Ce-ce-ku-ce a India kan asibitin da ya ce ba zai karbi musulmi ba

    'Yan sanda a India sun kai karar wani asibiti a kasar bayan da ya ce ba zai karbi musulmi ba.

    Asibitin dai ya wallafa wani talla a wata jarida inda ya ce ba zai karbi duk wani musulmi ba har sai suna da shaidar gwaji da ke nuna ba sa dauke da cutar korona.

    Wannan bayani dai ya janyo ce-ce-ku-ce a soshiyal midiya abin da ya janyo asibitin ya sake wallafa wani tallan a jarida na neman afuwa.

    Kimanin kaso 30 na masu dauke da cutar korona a India na da alaka da tarukan wa'azi na kungiyar musulmi ta Tablighi Jma'at.

    Tuni dai gwamnati ta ja kunnen rarraba kan jama'a ta hanyar addini.

  17. Covid-19: Amurka da kamfanin Novartis sun cimma yarjejeniya kan maganain Maleriya

    Kamfanin hada magunguna na Novartis ya cimma yarjejeniya da gwamnatin Amurka na ci gaba da amfani da maganin cutar Maleriya wato hydroxychloroquine a kan masu dauke da cutar korona 440.

    Shugaban Amurka, Donald Trump ne dai yake ta yekuwar yin amfani da maganin inda ya ce zai iya warkar da cutar korona.

    To sia dai babu wata shaida a kimiyyance da ke nuna hakan.

    Dakunan gwaji a fadin duniya dai na rige-rige wajen samar da rigakafin cutar ta korona.

  18. Coronavirus: An fara sassauta dokar kulle a Turai

    Kasashe da dama musamman a nahiyar Turai na daukan matakai daban-daban don sassauta matakan kulle da suka dauka.

    Daga yau Litinin, Poland za ta sake bude wuraren shakatawa sannan za a bude makarantun reno a Norway domin ci gaba da harkokin karatu ga yara.

    Ita ma jamhuriyar Czech (Check) za ta bude kasuwanni domin hada-hada sannan a Albania ma, masana'antun man fetur da na hakon ma'adinai za su sake budewa.

    Amma Spaniya, kasar da ta fi sanya tsauraran matakan kulle da Faransa sun amince su jinkirta matakin dage takunkuman zuwa nan da wasu karin makonni.

  19. Coronavirus: Jamus za ta sassauta dokar kulle

    A Yau ne Jamus za ta fara sassauta wasu daga cikin takunkuman da ta kakaba domin hana yaduwar cutar korona ciki har da bude wasu shaguna da makarantu.

    Hukumomi a kasar ta Jamus sun sanar tun makon da ya gabata cewa an samu raguwar masu kamuwa da annobar kuma ana samun galaba kan cutar.

    Amma duk da samun karuwar mutanen da suke mutuwa saboda cutar, hukumomin sun fadada matakan gwaje-gwaje da sa takunkumi a shaguna da wuraren shiga mota.

    Sai dai shugabar gwamnati Angela Merkel ba ta fito ta yi magana kan yadda jagororin jihohin kasar 16 za su aiwatar da sassaucin matakan ba.

  20. Alkaluman masu cutar korona na karuwa a Turkiyya

    Alkaluman baya-bayan nan daga Turkiyya na nuna cewa kasar a yanzu ta fi samun karin masu dauke da cutar korona sama da China - inda cutar ta samo asali.

    Kusan mutum 4000 ne suka kamu da cutar a kasar ta Turkiyya cikin kwana daya lamarin da ya kai yawan mutanen da suka harbu a kasar zuwa sama da 86,000.

    Sai dai Italiya ta samu raguwar yawan mutanen da suka mutu saboda cutar korona da kuma masu kamuwa da cutar.

    Mutum 433 ne suka mutu sakamakon cutar a Italiyan.

    Ita ma Faransa ta fara nuna alamun samun nasara kan annobar bayan da aka fi samun masu warkewa daga cutar kan wadanda ake kai wa asibiti.