Hotunan baraguzan gine-gine


Wannan shafin na kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da Kamaru da Chadi da ma sauran kasashen duniya har da rahotanni kan coronavirus.
Umar Mikail


Wani a shafin Twitter ya wallafa bidiyon yadda wannan lamari ya shafi abokinsa inda gidan da yake da kuma motocin gidan duk sun lalace.
Wannan labari ne na dauke da bayanai da X suka bayar. Muna neman amincewarku kafin mu dora muka, saboda nuna iya dauke da wasu bayanai da aka iya adanawa. Watakila kana za ka so ka karanta X da tsarin bayanan da za a adana da da tsarin sirri kafin ka amince. Idan kana son ganin wannan bayani ka zabi ‘amince sannan ka ci gaba’.
Karshen labarin da aka sa a X
Jami'an Kungiyar Red Cross sun tabbatar wa BBC da cewa an samu nasarar ceto mutum 15 a halin yanzu daga wata makaranta da gininta ya ruguzo kuma suna asibiti ana duba lafiyarsu.
Tuni wasu da ke zaune a Unguwar Abule Ado suka fara gudun hijira sakamakon firgicin da suka shiga a safiyar yau.


Jami'an hukumur tsaro ta NSCDC sun isa wurin da lamarin ya faru.
A halin yanzu suna bincike da kuma duba yadda abubuwa suke kuma ana sa ran za su yi karin bayani.
Wasu mazauna wannan wuri sun shaida cewa akwai gwamman mutane da ba a ceto ba wadanda ke ciki wani hali.
An samu nasarar ceto wata mata da kuma wasu dalibai uku inda tuni aka wuce da su asibiti domin duba lafiyarsu.
Motar kashe gobara kenan za ta koma debo ruwa domin a ci gaba da kashe wuta

Rahotanni daga jihar Legas na cewa an samu fashewar bututun mai a Unguwar Abule Ado a jihar da ke kudu maso yammacin Najeriya
Gajimarin hayaki ya turnike sararin samaniya bayan afkuwar lamarin.
Wakilanmu da ke Legas din sun shaida mana cewa gidaje da dama ne suka rushe kuma yanzu haka babu cikakken bayani dangane da rayukan da suka salwanta sakamakon wannan iftila'i.
Tuni dai jami'an bayar da agajin gaggawa ciki har da kungiyar Red Cross International suka garzaya wurin domin bayar da agaji.
Masu bibiyarmu barkanmu da wannan rana ta Lahadi, wannan shafin zai kawo muku rahotanni da kuma labarai kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da wasu sassan duniya, a ci gaba da kasancewa tare da mu.