Mutum biyar sun mutu a harin Gwoza, Wasu mutum tara kuma sun jikkata kuma suna samun kulawa a asibiti.

Asalin hoton, Getty Images
Yawan mutanen da suka rasu a harin kunar bakin wake da ake kai garin Gwoza a jihar Bornon Najeriya ya karu zuwa biyar, a cewar ma’aikatan ceto.
Wasu mutum tara kuma sun jikkata kuma suna samun kulawa a asibiti.
Mamatan sun hada da da wasu mutum biyu da suka mutu nan take da wani mutumin da ya mutu a asibiti sai kuma ‘yan mata biyu da suka kai harin. Wadanda suka samu raunuka kuma na samun kulawa.
Rahotanni da aka samu da farko sun ce ‘yar kunar bakin waken ta tayar da bam din da ke nade a jikinta ba bayan kutsa cikin masallatan da ke sallar Subahi.
Babu wata kungiya da ta iya ikirarin kai harin amma kungiyoyin Boko Haram da ta ISWAP sun saba kai hare-hare ayankin.


