DSS ta bankado shirin 'tayar da hargitsi' lokacin Kirsimati a Najeriya
Hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya ta ce ta gano wasu shirye-shirye da wasu gungun mutane ke yi da ke nufin haifar da yamutsi a sassan kasar ciki har da babban birnin kasar Abuja.
Shirin na ingiza mutane su fito zanga-zanga da kuma haifar da hargitsi da tashin hankali don tabarbara al’amura a kasar.
Cikin wata sanarwa da Peter Afunanya jami'in hulda da jama'ana hukumar DSS ya fitar ta ce ta bankado shirin wadda aka tsara gudanar da tashin hankali a manyan biranen shiyoyin Najeriya cikin makonni masu zuwa.
Masu wannan shirin son aiwatar da wannan mugun nufin ne a lokutan bukukuwan Kirsimati a cewar sanarwar.