Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

DSS ta sake kama Sowore

Wannan shafi ne da ke kawo maku rahotanni kai-tsaye game da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da Kamaru da Ghana da wasu makwabtansu a yau.

Rahoto kai-tsaye

Fauziyya Kabir Tukur and Umar Mikail

  1. An yanke wa Sanata Orji Kalu hukuncin dauri shekara 12

    Wata babbar kotu a Legas ta yanke wa sanata mai ci kuma tsohon gwamnan jihar Abia, Orji Uzo Kalu hukuncin zama a gida kaso tsawon shekara 12 bisa zargin almundahanar Naira biliyan 7.65.

    Mai shari'a Mohammed Idris ya bayyana cewa an kama sanatan da laifin da ake zarginsa da shi, kuma an kwashe tsawon shekara 12 ana shari'ar.

    An yi sharia'r Mista Kalu tare da kamfaninsa Slok Nigeria Limited ne da kuma Darektan harkokin kudi na gidan gwamnatin jihar Abia a lokacin da Mista Kalu ke gwamna, Udeh Udeogu.

  2. Kamaru, Lauyoyi a Kamaru za su shiga yajin aiki

    Lauyoyi a yankin renon Ingila na yunkurin kaurace wa kotuna da fita tituna su yi zanga-zanga don nuna rashin amincewarsu kan wasu kudurorin doka biyu da gwamnati ke shirin shigarwa majalisar dokoki.

    Daya daga cikin dokokin za ta bai wa ko wane alkali a Kamaru damar yanke hukunci a kotun soji da kotu ta musamman ta manyan laifuka alhalin kuma yankin renon Ingila na amfani da tsarin dokoki ne na tsarin shari'a mai amfani da dokokin kunne ya girmi kaka, wato "common law" sabanin yankin Faransanci mai amfani da tsarin shari'a mai amfani da rubutattun dokoki, wato "civil law".

    Dokar karshe kuma ta shafi malaman jami’a wadanda za su samu damar yin bitar karatu a dukkanin jami’o’i na sassan kasa da za a iya aika su.

    Wannan sabanin tsakanin amfani da harsunan biyu ne musamman ta bangaren lauyoyi, shi ne masabbabin abinda ya haifar da rikicin da ake ciki a yanzu a yankin rainon Ingila tsawon shekara hudu kenan.

    �o

  3. Gobara ta tashi a kusa da rukunin gidajen Diamond Estate a Legas

    Gobara ta tashi a kusa da rukunin gidajen Diamond Estate da ke kan titin Isheri/Lasu -Igando.

    Rahotanni na cewa gobrara ta tashi ne sakamakon fasa bututun man fetur.

  4. 'Yan Najeriya na nemar wa matar da ''aka ki ba ta taimako a asibiti'' hakkinta

    'Yan Najeriya ne neman a bi wa wata mata hakkinta wacce ''ta mutu a asibiti bayan da suka ki duba ta'' sakamakon caka mata wuka da aka yi a wuya.'

    Asibitin sun yi watsi da zargin da ake musu na kin kula da ita.

    Rahotanni sun ce wani barawo ne ya caka wa Moradeun Balogun wuka a wuya a kan hanyarta ta koma wa gida.

    An garzaya da ita asibiti inda ta yi ta zubar da jini har ta mutu.

    'Yar uwar marigayiyar Molad, ta ce asibitin sun ki karbarta don duba ta suka ce sai an kawo rahoton 'yan sanda.

    Sai dai asibitin da aka kai Ms Balogun sun ce ba su ki karbarta ba.

    Daraktan Asibitin Jolad, Funso Oladipo ya shaida wa Jaridar Premium Times cewa likitoci sun karbi Ms Balogun amma sai suka fahimci cewa tana bukatar dubawar kwararru.

    ''Ba mu karbe ta a asibitin ba. Nan da nan muka mayar da ita Gbagada bayan da muka fahimci cewa ba za mu iya ba ta taimakon da take bukata ba kuma wadanda suka kawo ta sun yi tafiyarsu,'' a cewarsa.

    Sai dai 'yan Najeriya suna ta magana a shafukan sada zumunta cewa an ki a duba ta ne, sannan batun nemar mata hakkinta na ci gaba da tashe.

    Ana ta amfani da maudu'in #JusticeForMoradeun, abokai da iyayen marigayiya Moradeun Balogun sun zargi asibitin da nuna halin ko in kula.

  5. 'Yan bindiga sun kashe dan canji a Abuja

    Rahotanni daga Abuja babban birnin Najeriya na cewa 'yan bindiga sun harbe wani mutum a wajen 'yan canjin kudi da ke unguwar Zone 4.

    Wasu ganau sun shaida wa BBC cewa wasu mutum biyu ne suka zo a kafa suka bukaci za su yi canjin kudi, ''ya kawo musu kudin kenan sai ga wata mota ta tsaya, wani ya fito da bindiga ya kwace kudaden ya kuma harbe shi a kirji da kai,'' in ji ganau din.

    Ya kara da cewa ''Da yin hakan sai suka shige mota suka gudu.'' Al'amarin ya faru ne da safiyar Alhamis da misalin karfe 9.

    Wajen da lamarin ya faru waje ne na hada-hadar jama'a kuma a tsakiyar babban birnin yake. Tuni dai aka dauki gawar mamacin zuwa asibiti a cewar abokan aikinsa.

  6. Masu bin mu a wannan shafi Assalamu Alaikum!

    Ku kasance da mu a yau don karanta labaran abubuwan da ke wakana a najeriya da Nijar da Kamaru da Ghana da Chadi sa ma sauran kasashen da ke makwabtaka da su.

  7. Ban kwana

    Masu bibiyarmu nan muka kawo karshen rahotannin kai-tsaye.

    Ku duba kasa domin karanta abubuwan da suka faru a Najeriya da makwabtanta a yau Laraba zuwa yanzu da muke rufewa.

    Za ku iya ci gaba da karanta sauran labarai a sauran shafukanmu.

    Muna kara gode maku da kasancewa tare da mu.

  8. Majalisar Kano ta kasa cimma matsaya kan dokar sabbin masarautu

    Zaman da majalisar dokokin jihar Kano ta yi a yau kan duba dokar kirkiro sabbin masarautu ya tashi ba tare da cimma matsaya ba.

    Yayin zaman, 'yan majalisar sun yi muhawara kan dokar har na tsawon sa'a uku a kebe ba tare da 'yan jarida ba.

    Sai dai ba su samu yadda suke so ba, yayin da suka yi yunkurin yi wa dokar karatu na biyu a yau din biyo bayan kammala karatu na farko.

    Sai dai sun ci alwashin ci gaba da duba dokar a zamansu na gobe Alhamis.

    A gefe guda kuma, wasu daga cikin 'yan majalisar jam'iyyar adawa ta PDP a jihar sun yi yunkurin sukar dokar a zauren majalisar amma hakarsu ba ta cimma ruwa ba, inda suka rika daga hannu amma aka hana su damar yin magana ba.

    PDP tana da 'yan majalisa 12 ne kacal cikin 40 a majalisar, abin da ke nufin ba za su iya kawo tsaiko ga dokar ba saboda ba su kai biyu bisa uku ba, wanda shi ne yawan 'yan majalisar da doka ta tanada su amince kafin yin wata doka.

    Idan za a iya tunawa dai a ranar 21 ga Satumban 2019 ne Mai Shari'a Usman Na’abba na babbar kotun jihar Kano ya soke dokar farko da majalisar ta yi na kirkiro masarautun Karaye da Gaya da Bichi da Rano, inda ya ce ba a bi ka'ida ba yayin yin ta.

    Daga nan ne kuma 'yan majalisar suka daura aniyar sake yin dokar ta hanyar da ta dace bisa kudirin da gwamnati ta aike masu. A baya dai cikin kwana daya aka kai kudiri kuma aka kaddamar da dokar.

  9. Buhari ya koma Abuja, ya kaddamar da daftarin tsaro

    Shugaba Muhammadu Buhari ya kaddamar da wani daftarin tsaro na kasa baki daya da aka kira shi da National Security Strategy 2019, wanda kuma ofishin mai bai wa shugaban shawara kan harkar tsaro ya samar.

    Bayan haka ne kuma Buhari ya jagoranci zaman majalisar zartarwa wato Federal Executive Council kamar yadda aka saba duk ranar Laraba.

    Duk wannan ya faru ne jim kadan bayan ya koma birnin tarayya Abuja daga ziyarar aiki da ya kai jihohin Katsina da kuma Kaduna.

    A wurin taron ne kuma Buhari ya jaddada yunkurin gwamnatinsa na inganta harkar tsaro a Najeriya.

  10. EFCC ta gurfanar da 'Mama Boko Haram' a gaban kotu

    Hukumar yaki da cin hanci a Njaeriya EFCC ta gurfanar daTahiru Saidu Daura da Barista Aisha Alkali Wakil, wadda ake yi wa lakabi da Mama Boko Haram, a gaban kotu bisa zarginsu da laifin zambar kudi naira miliyan 66.

    Hukumar ta ce mai Shari'a Aisha Kumaliya ce ta babbar kotun jihar Borno ce za ta jagoranci shari'ar a yau Laraba, inda ake zarginsu da laifuka har uku.

    Mamallakin kamfanin AMTMAT Global Ventures mai suna Ali Tijjani ne ya yi korafi kan gidauniyar Complete Care and Aids Foundation, wadda Mama Boko haram ke jagoranta, bisa zargin zamba kan biski da ya samar wa gidauniyar.

    Sai dai jaridar Daily Trust a Najeriya ta ruwaito cewa tuni kotun ta yi zaman kuma har an bayar da belin Aisha Alkali Wakili kan kudi naira milyan 30, amma saboda rashin halartar wadanda ake zargin kotun ta ce za ta dage bayar da belin.

    Barista Aisha Alkali Wakil ta taka rawa yayin tattaunawar sulhu tsakanin kungiyar Boko Haram da gwamnatin Najeriya, abin da ya sa ake yi mata lakabi da Mama Boko Haram.

  11. Za a biya Sarki Sanusi diyya

    Hukumar da ke kula da filaye ta jihar Kano ta yi watsi da wasu rahotanni da ke cewa gwamnatin jihar ta kwace filin Sarki Muhammadu Sanusi wanda aka kimanta kudinsa ya kai Naira miliyan 250 kuma a cewar rahotannin an biya Sarkin diyyar Naira miliyan 4.5.

    A wata sanarwa da kakakin hukumar, Murtala Shehu Umar ya fitar ya ce gwamnatin jihar ba ta kwace filin Sarkin ba.

    Ya kuma ce duk da cewa gwamnatin Gwamna Abdullahi Umar Ganduje na gina babbar gada, irinta ta farko a kasar, kuma saboda yanayin tsarinta da girmanta za a rusa wasu gine-gine a kusa da ita.

    Cikin gine-gine da aka rusa har da wata katanaga da ta kewaye filin sarkin kuma da saninsa da izininsa aka rusa katangar, amma ba a taba filin ba.

    Sanarwar kuma ta bukaci Sarkin da ya aika wa hukumar lambar asusun ajiyarsa ta banki don gaggawar biyansa diyyar katangarsa.

  12. Mutum miliyan 4.1 a Zimbabwe za su samu tallafin abinci

    Kusan kashi biyu cikin hudu na 'yan kasar Zimbabwe ne za su samu tallafin abinci daga Majalisar Dinkin Duniya a yaunkurinta na hana kasar fadawa cikin kangin yunwa.

    Hukumar Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya, World Food Programme (WFP), ta ce za ta samar wa mutum miliyan 4.1 da kayan kanti da kuma tsaba, kamar wake, da kuma man girki.

    Kusan rabin al'ummar kasar suna fuskantar barazanar yunwa, yayin da kusan miliyan 7.7 suke cikin yunwar.

    Sama da tan 240,000 na kayan abinci za a raba domin rage radadin yunwar, wanda WFP za ta aiwatar.

  13. WAEC ta janye sakamakon jarrabawar wasu daliban shekarun 1992 da 1993

    Hukumar Shirya Jarrabawar Kammala sakandire ta Africa ta Yamma, WAEC, ta fitar da jerin sunayen wasu da suka zana jarabawar, wadanda ake tunanin cewa sun yi magudi a jarabawar da aka yi a watan Disambar 1992 da 1993.

    Jaridun Najeriya da dama sun ruwaito cewa an buga jerin sunayen ne a sanarwar Hukumar shirya jarabawar shiga manyan makarantu ta JAMB ta mako-mako da aka fitar ranar Litinin.

    Hukumar ta fitar da lambobin takaddun shaidar zana jarabawar, tare da bayyana cewa sun yi amfani da sojan haya wajen rubuta jarabawar.

  14. Chadi, 'Bai dace a sako Hissène Habré ba'

    Wadanda suka fuskanci ukubar tsohon Shugaban Chadi Hissène Habré sun nuna damuwarsu kan abin da suka ce kamfe ne na son a sako wanda ya yi mulkin kama karyar.

    Habre ya jagoranci kasar daga 1982 zuwa 1990, kuma wata kotu a Senegal ta kama shi da laifin yaki da azabtar da mutane a shekatar 2016 sannan tayanke masa hukuncin daurin rai da rai.

    Daya daga cikin mutanen da Habre ya azabtar, Clement Abaifo ya shaida wa BBC cewa ba zai dace a saki Habre ba.

    Matar habre, fatima Raymonne ta shaida wa gidan radiyon RFI a cikin watan jiya cewa tsohon shugaban ba shi da lafiya kuma jami'an gidan yari sun ki kula shi lokacin da ya fadi a bayan gida.

    A cewarta, maigidan nata ya shaida mata haka ne ta hanyar kiranta a wayar da aka ba shi bayan da ya samu ciwon bugun zuciya kuma sai bayan ya kira ta a wayar ne hukumomin gidan yari suka kula da shi.

  15. Kamaru, Malaman jami'a za su shiga yajin aiki

    Ana sa rai malamai a Jami'ar Bamenda za su fara yajin aiki a yau, don nuna bacin ransu da kuma bukatar hukumomi su dauki mataki bisa rashin tsaro da ke addabar yankin.

    Kwanan nan ne aka sace wani farfesa a jami'ar kuma har yanzu akwai rashin jituwa tsakanin gwamnati da 'yan awaren yankin rainon Ingila a yankin.

  16. Ghana, An umarci MTN ta biya kwastomominta diyya

    Hukumomi a Ghana sun umarci kamfanin waya na MTN kan ya biya diyya ga kwastomominsa da suka fuskanci matsala dalilin lalacewar wasu na'urorin kamfanin a farkon wannan makon, don tabbatar da cewa kamfanin ya biya duka kudin da ya cire wa masu amfani da layin bisa kuskure.

    Ana ta ce-ce-ku-ce musamman a shafukan sada zumunta kan wahalar sayen data, yayin da wasu suka fusata kan tsadar datan.

  17. Ana son a hada dala miliyan 100 don taimaka wa Nijar da Mali da Burkina Faso yakar ta'addanci

    Mambobin Kungiyar Kasashen Afirka Ta Yamma da ke amfani da kudin CFA (UEMOA) sun roki da a yi gaggawar hada tallafin dala miliyan 100 don taimaka wa Burkina Faso da Mali da Nijar a yakin da suke da ta'addanci.

    An yi wannan rokon ne a ranar Talata bayan kammala taron kungiyar ta UEMOA, gabanin taron shugabannin kasashen yankin a Dakar.

    Mali da Burkina Faso da Nijar na daga cikin mambobin kasashen G5 na yankin Sahel da ke yaki da ta'addanci, wadda ke kokarin kawo karshen ta'addanci a yankin.

  18. Kotu ta umarci tsoffin gwamnoni su dawo da fanshonsu

    Wata babbar Kotun tarayya a Legas ta bai wa gwamnatin Najeriya umarnin karbo kudaden fansho daga tsoffin gwamnoni da yanzu suka zama ministoci da ‘yan majalisa.

    Jaridar Punch ta ruwaito cewa wasu daga cikin wanda abin ya shafa sun hada da tsohon shugaban majalisar dattijai kuma tsohon gwamnan jihar Kwara, Bukola Saraki, tsohon gwamnan Akwa Ibom kuma ministan yankin neja Delta, Godswill Akpabio, gwmanna Ekiti, Kayode Fayemi da ministan ayyuka da gidaje kuma tsohon gwamnan Legas Babatunde Fashola da dai sauransu.

  19. Masu bin mu a wannan shafi barkanmu da safiya!

    Ku biyo mu don karanta labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da Kamaru da Chadi da Ghana da sauran makwabtan kasashe a yau.

  20. Karshe! Ku karanta labaran Talata daga nan zuwa kasa, Za mu dawo gobe Laraba da sabbin labarai

    Wannan muka kawo karshen wannnan shafi wanda ya kawo maku rahotanni kai-tsaye kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da Nijar da Kamaru da Ghana da wasu makwabtansu.

    Sai kuma gobe, idan Allah Ya kai mu. Mun gode.