Shari'ar Buhari da Atiku
Kuna iya kallon yadda shari'ar ke gudana kai-tsaye a Facebook a BBC Hausa.
Kotun sauraron kararrakin zabe a Najeriya ta yi watsi da karar da tsohon mataimakin shugaban kasar, Atiku Abubakar, ya shigar a gabanta, yana kalubalantar zaben Shugaba Muhammadu Buhari.
Umar Mikail
Kuna iya kallon yadda shari'ar ke gudana kai-tsaye a Facebook a BBC Hausa.

Asalin hoton, Others

Asalin hoton, Nigeria Presidency
Harabar kotun kenan yayin da lauyoyin da ke wakiltar bangarorin biyu ke ci gaba da jiran hukunci.

Asalin hoton, Channels TV


Alkalai biyar din da za su yanke hukunci a zaman kotun na yau sune:
·Mai Shari’a Abdul Aboki daga Abuja
·Mai Shari’a Joseph Ikyegh daga Benin
·Mai Shari’a Samuel Oseji daga Legas
·Mai Shari’a Peter Ige daga Abuja
·Mai Shari’a Muhammad Garba
Tuni kotun ta cika da manya-manya daga jam'iyyun guda biyu, yayin da kowane bangare ke sanin makomarsa a yau din.



Yau Laraba kotun sauraron kararrakin zabe take yanke hukunci dangane da karar da Atiku Abubakar na jam'iyyar PDP ya shigar a gabanta ta kalubalantar zaben Shugaba Muhammadu Buhari na jam'iyyar APC.
Atiku Abubakar ya shigar da karar ne bayan da hukumar zaben kasar INEC ta bayyana Shugaba Buhari a matsayin wanda ya ci zaben ranar 23 ga watan Fabrairun wannan shekara ta 2019.
Masu bibiyarmu barkanku da safiyar Laraba, Umar Mikail ke maku fatan an tashi lafiya.
Za mu kawo maku rahotanni kai-tsaye game da hukuncin kotun sauraron kararrakin zabe a Najeriya tsakanin jam'iyyun APC mai mulki da kuma PDP mai adawa.