PDP ta nemi a soke zaben Osun

Labarai da sharhi game da karashen zaben gwamnan Osun inda dan takarar jam'iyyar PDP da na APC suka kara.

Rahoto kai-tsaye

Abdulwasiu Hassan

  1. An fara kada kuri'a a Osogbo

    Osogbo
    Bayanan hoto, An fara kada kuri'a a Osogbo

    An fara kada kuri'a a karamar hukumar Osogbo ne da misalin karfe takwas da minti biyar.

  2. An fito sosai

    Rumfar zabe ta biyar a mazaba ta 17
    Bayanan hoto, A rumfar zabe ta biyar a mazaba ta 17 a garin Osogbo mutum 884 suka yi rijista kuma mutum 667 ne suka karbi katin zabensu.

    Mutane sun fito sosai domin kada kuri'u a rumfunar zabe bakwai din da ake zaben a yau.

  3. Masu zabe suna duba sunayensu a rijista

    Masu zabe
    Bayanan hoto, Da sanyin safiyar ranar Alhamis ne dai masu zabe suka fara duda sunayensu a rijista.
  4. Barka da shigowa

    Jama'a, barkanku da shigowa wannan shafi inda za mu kawo muku yadda ake karasa zaben gwamnan jihar Osun da aka fara ranar Asabar.

    Ranar Lahadi ne dai hukumar zabe ta INEC ta yanke hukuncin cewar ba a kammala zaben ba, kuma za a karasa zabe a wasu rumfunar zabe bakwai da ba a yi zabe ba ko kuma aka soke zabensu.