Yaƙin Iran da abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sassan duniya

Wannan shafi ne da ke kawo muku irin wainar da ake toyawa a yaƙin da Amurka da Isra'ila ke yi a kan Iran da sauran abubuwan da ke faruwa a sassan duniya na ranar 27/04/2026

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Ibrahim Haruna Kakangi da Aisha Aliyu Jaafar da Abdullahi Bello Diginza

  1. Ƴan bindiga sun kashe Ministan tsaron Mali Sadio Camara

    Sadio Camara

    Asalin hoton, Reuters

    Ministan tsaron Mali, Sadio Camara, ya rasu sakamakon wani harin ƙunar baƙin wake da aka kai gidansa da ke kusa da babban birnin ƙasar, Bamako, a ranar Asabar.

    Harin na ɗaya daga cikin jerin hare-hare da masu ɗauke da makamai da kuma ‘yan awaren Tuareg suka kai a wasu birane daban-daban a lokaci guda.

    Wakilin BBC ya ce tsawon gwamman shekaru kenan ƴan awaren na Tuareg da a aka fi sani da FLA ke ta ƙokarin ɓallewa don kafa na su shugabancin, a wannan yanki, lamarin da ya sa suka haɗa kai da ƙungiyar JNIM mai akala da Alqa'eda wadda ita kuma manufarta ita ce yana manufarta a yankin wajen kai waɗannan hare hare.

    A yanzu dai ƴan tawayen na Tuareg sun ce suna riƙe da garin Kidan, mai muhimmanci na yankin hamada, inda wata rundunar tsaron Rasha ke da sansani.

    Haka kuma an kai hari gidan shugaban mulkin sojin kasar Assimi Goïta, amma bai samu wani rauni ba.

  2. Wakilin Iran ya isa Rasha domin ganawa da Putin

    Araqchi na gaisawa da jami'an Rasha

    Asalin hoton, TELEGRAM/REUTERS

    Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi, ya isa birnin St Petersburg domin tattaunawa da shugaban Rasha, Vladimir Putin.

    Rahotannin kafafen watsa labaran Amurka sun ce Iran ta gabatar da wani sabon shiri ga Washington, wanda ya mayar da hankali kan buɗe mashigin Hormuz, da kuma kawo ƙarshen yaƙin, wanda kuma ya buƙaci ɗage tattaunawar nukiliya zuwa wani lokaci na gaba.

    Tun da farko, Mista Araghchi ya ce tattaunawarsa a ƙasar Oman a ranar Lahadi ta mayar da hankali kan hanyoyin tabbatar da zirga-zirgar jiragen ruwa ta mashigin.

    Sai dai Shugaba Donald Trump ya ce dole ne duk wata yarjejeniya ta ƙunshi buƙatar Iran ta yi watsi da duk wani yunƙuri na ƙera makamin nukiliya.

  3. Buɗewa

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da shiga sabon mako.

    A yau Litinin ma mun shirya tsaf domin kawo muku labarai kan halin da duniya ke ciki.

    Ku biyo mu a shafukanmu na sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa, har ma ku kalli bidiyon da muka wallafa.