Ƙungiyar ɗaliban FGC Kano sun koka kan ƙoƙarin mamaye filayen makaranta
Ƙungiyar tsofaffin ɗaliban kwalejin tarayya da ke Kano ta yi kakkausar suka kan abin da ta kira haramtaccen cin iyakar fili mallakar kwalejin tarayya da ke Kano.
Al'amarin dai ya janyo damuwa a tsakanin tsaffin ɗaliban game da tsaron kadarorin ilimi na ƙasa.
Kungiyar ta bayyana cewa ta ɗauki matakai cikin gaggawa domin shawo kan lamarin, ciki har da matakan shari’a, amma a cewarsu ana ci gaba da aikin yanka filayen da gine-gine.







