Ƴan sanda a Ghana sun ce sun kama mutum 12 waɗanda ake zargi da sata da kuma lalata wuraren ajiye kayayyaki a wasu sassan ƙasar.
Mai magana da yawun ƴan sandan ƙasar, ACP Grace Ansah-Akrofi, ta ce bincike ya nuna cewa mutanen da ake zargin sun kai hari tare da lalata kayayyaki.
Wuraren da suka lalata sun haɗa da ofishin hukumar zaɓen ƙasar a mazaɓar Damongo da ke yankin Savannah.
Sun kuma lalata gidajen wasu shugabanni al'ummomi a sassan ƙasar, har ma da wasu cibiyoyin tattara sakamakon zaɓe.
"Wasu daga cikin mutanen da muke zargin, sun kutsa cikin rumbun ajiye abinci na ɗalibai a Tamale tare da yin awon gaba da kayan abinci," in ji kakakin ƴan sandan.
Ƴan sanda sun buƙaci mutane su kwantar da hankali yayin da suka aika jami'an tsaro zuwa muhimman wurare domin yin sintiri da mayar da doka da oda.