Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 08/12/2024

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 08/12/2024

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Abdullahi Bello Diginza da Ahmad Bawage

  1. Zaɓen Ghana: Ministan cikin gida ya rasa kujerarsa ta ɗan majalisa

    Ministan cikin gida na Ghana, Henry Quartey na jam'iyyar NPP mai mulki ya rasa kujerarsa ta ɗan majalisar gundumar Ayawaso ta Tsakiya.

    Kafin naɗa shi muƙamin ministan, Mista Quartey shi ne ministan jihar Greater Accra

    Ɗan takarar jam'iyyar NDC mai hamayya, Abdul Rauf Tubazu ne ya kayar da shi a mazabar tasa, kamar yadda sakamakon da hukumar zaɓen ƙasar ta bayyana ya nuna.

    Ga yadda sakamakon hukumar zaɓen ƙasar ya nuna:

    • Henry Quartey (NPP) - 23,345
    • Abdul Rauf Tubazu (NDC) - 29,755
    • Charles Kwame Adams (NDP) - 163

    Jim kaɗan bayan bayyana sakamakon zaɓen gundumar, ɗan takarar NDC da ya yi nasara ya ce tuni dama yana da ƙwarin gwiwar lashe zaɓen.

  2. 'Firaministan Syria na son shirya zaɓe domin mutane su zaɓi sabbin jagorori'

    Firaministan Syria, Mohammed Ghazi al-Jalali ya ce ƙasar za ta shirya sahihi kum ingantaccen zaɓe cikin wata hira da kafar yaɗa labarai ta Al-Arabiya, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ambata.

    Ya kuma ce ya yi magana da kwamandan 'yantawayen, Abu Mohammed al-Jawlani dangane da lokacin miƙa mulkin.

    Da safiyar yau ne kafar yaɗa labarai ta Al-Arabiya ta ambato firaministan na cewa bai yi magana da shugaba Bashar al-Assad ba tun 'jiya da yamma' kuma bai san inda shugaban ya shiga.

    Da safiyar yau ne firaministan ya yi gabatar da jawabi ga ƙasar ta shafinsa na sada zumunta.

    Inda a ciki ya ce a shirye yake ya taimaka wajen yin abin da ya dace a ƙasar.

  3. Jam'iyyar NDC mai hamayya na kan gaba a sakamakon zaɓen Ghana - rahotonni

    Rahotonni daga ƙasar Ghana na nuna cewa jam'iyyar NDC mai hamayya ta tsohon shugaban ƙasar John Mahama na kan gaba a sakamakon zaɓen ƙasar da ake tattarawa.

    Sakamakon da gidan talbijin na ƙasar GBC, ya wallafa kawo yanzu ya nuna cewa ɗan takarar hamayyar, na da kashi 60.7 cikin 100 yayin da NPP mai mulki ke da kashi 37.6 na ƙuri’un da aka tattara ya zuwa yanzu.

    Haka kuma gidan talbijin ɗin na GBC ya ce kawo yanzu jam'iyyar NDC na da kujerun majalisa 17 yayin da NPP ke da 5.

    Ƙasar Ghana na da jihohi 16 tare da gundumomin 'yan majalisa 275. Hukumar zaɓen ƙasar, EC ce dai kaɗai ke da alhakin sanar da sakamakon zaɓen ƙasar.

  4. 'Yantawayen Syria sun gabatar da jawabin nasara a gidan talbijin na ƙasar

    'Yantawayen Syria sun gabatar da jawabi kai tsaye a gidan talbijin na ƙasar da kuma gidan radiyon Damascus, inda suka yi iƙirarin kawo ƙarshen gwamnatin Bashar al-Assad tare da sakin fursunonin siyasa.

    Mayaƙan tawayen da suka bayyana a talbijin ɗin sun yi kira ga mambobinsu da suka kira ''mujahidai'' da sauran 'yan ƙasa su kauce wa ɓarnatar da dukiyar gwamnati.

    Cikin daren da ya gabata ne da 'yantawayen suka ƙwace iko da Damascus, babban birnin ƙasar, bayan ƙwace wasu manyan biranen ƙasar.

  5. Ana ci gaba da ƙidaya ƙuri'u a zaɓen shugaban ƙasar Ghana

    Ana ci gaba da ƙidaya ƙuri'u a zaɓen shugaban ƙasa da na 'yan majalisa a Ghana bayan gudanar da zaɓen a cikin kwanciyar hankali.

    Ana sa ran fara samun sakamakon wucin-gadi na zaɓen daga yau Lahadi.

    'Yan sanda sun ce mutum guda ya rasu sakamakon harbin bindiga a arewacin ƙasar lokacin wani rikicin zaɓe.

    Matsawar babu ɗan takarar da ya samu fiye da kashi 50 cikin 100 na ƙuri'in da aka kaɗa to za a je zagaye na biyu a zaɓen.

  6. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa barkanmu da hutun ƙarshen mako.

    Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci domin ci gaba da kawo muku irin wainar da ake toyawa a faɗin duniya.

    Kuna iya leƙawa shafukan sada zumunta domin tafka muhawara kan labaran da muke wallafawa.