Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 06/10/2025.

Wannan shafi ne da ke kawo abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 06/10/2025.

Rahoto kai-tsaye

Daga Habiba Adamu da Aisha Babangida

  1. Waɗanda suka mutu a makarantar Indonesia sun kai 54

    ....

    Asalin hoton, EPA

    Adadin waɗanda suka mutu a ginin makarantar da ta rushe a ƙasar Indonesia, sun ƙaru zuwa 54, a cewar hukumomi.

    Yayin da ake ci gaba da neman wasu gwammai.

    Ɗaruruwan dalibai ne, mafiya yawansu maza 'yan shekara goma sha ne, suka taru domin sallar jam'i, a makarantar kwana da ake koyar da ilimin addinin musulunci, Al Khoziny da ke gabashin Java, a lokacin da ginin ya rushe a ranar Litinin da ta gabata.

    Lamarin ya faru ne yayin da ake ci gaba da ginin makarantar.

    Hukumar kare bala'oi ta ƙasar ta ce, lamarin shi ne mafi muni da aka samu a wannan shekarar.

    Ana sa ran masu ceto za su zaƙulo wasu mutum 13 da baraguzan ginin ya binne.

    Masu bincike na neman gano musabbabin rushewar ginin. Yayin da wasu ke cewa ginin mai hawa biyu ya rufta ne saboda ba a yi mishi tushe mai ƙwari ba.

  2. Kwalara ta kashe mutane 4,778 a Najeriya

    .........

    Aƙalla, mutane 4,778 ne suka rasa rayukansu sakamakon cutar kwalara a Najeriya, tsakanin shekarar 2020 and 2024, a cewar hukumar yaƙi da cututtuka masu yaɗuwa a ƙasar(NCDC).

    Alƙaluman hukumar sun nuna cewa a shekarar 2020, mutum 3,513 ka yi zaton sun kamu da cutar, kuma a cikinsu mutum 95 sun mutu.

    Sai dai alƙaluman sun ƙaru matuƙa a shekarar 2021, inda aka yi zaton mutane 111,062 suka kamu da cutar, kuma 3,604 suka mutu a jihohi 33 na ƙasar.

    A shekarar 2025 kaɗai fiye da mutane 300 ne suka mutu, ciki har da mutuwar mutane 179 da sanarwar gwamnatin jihar Zamfara ta ce sun mutu a jihar cikin mutum 12,052 da ake zaton sun kamu da cutar a watan Satumba na 2025.

    Mataimakin gwamnan jihar Bauchi, Auwal Mohammed Jatau ya tabbatar da mutuwar mutum 58 cikin mutane 258 da ake zaton sabbin kamuwa ne da cutar ta kwalara a ƙananan hukumomi 14 na jihar.

    Mataimakin gwamnan ya bayyana hakan ne makonni biyu da suka gabata, kamar yadda jaridar Daily Trust ta wallafa.

    Hakan na faruwa ne duk da miliyoyin dalolin da ƙasar ta samu bashi daga babban bankin duniya don samar da ruwa, muhalli mai tsafta da kuma wasu tallafin dalar Amurka miliyan biyu da ƙasar ta samu daga Majalisar Ɗinkin Duniya don samar da rigakafin kwalara.

  3. Hamas da Isra'ila za su tattauna a Masar

    ,,,,,

    Asalin hoton, Reuters

    A ranar Litinin ne masu shiga tsakani daga Isra'ila da kuma Hamas za su yi tattaunawar da ba ta ƙeƙe da ƙeƙe ba a Masar, da nufin kawo ƙarshen yaƙin Gaza.

    Ganawar na zuwa ne bayan Hamas ta amince da wasu sassa na shirin zaman lafiya na shugaba Donald Trump.

    Akwai abubuwa da dama a yarjejeniyar da sai sun samu wucewa, don haka ana fargabar komi zai iya faruwa.

    Shugaban Amurka, Donald Trump ya ce an yi tattaunawa mai kyau a karshen mako game da sako sauran mutanen da Hamas ke riƙe da su.

    Ya buƙaci Isra'ilar da Hamas su yi gaggawar cimma matsaya yana mai gargaɗin abun da ka iya faruwa idan hakan ya gagara.

  4. A ba mu makamai don kare kanmu - Jama'ar Sokoto

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Al'ummar ƙaramar hukumar Kebbe ta jihar Sokoto a Arewa maso yammacin Najeriya ta buƙaci gwamanti ta basu ikon mallakar makamai domin kare kansu daga hare-haren ƴan bindiga da suka addabe su.

    Jama'ar yankin sun ce sun gaji da yadda ƴan bindigar ke ci gaba da kai masu hari, da kashe masu mutane da kuma garkuwa da wasu, lamarin da ya janyo masu mummunar asara.

    Sun ce daga cikin garuruwa 17 da ƙaramar hukumar Kebbe ke da su, a yanzu ƴan bindiga sun kori mutane daga garuruwa aƙalla 11, saboda yawaitar hare-hare.

    Tukur Muhammad Fakum, daya daga cikin jagororin al'ummar ya shaida wa BBC cewa an riga an kai maƙura, don haka a yanzu fatan su kawai bai wuce neman wa kai mafita ba.

  5. Assalamu Alaikum

    Barkanmu da sake saduwa a shafin labarai kai-tsaye na BBC Hausa a hantsin Litinin

    Shafin na yau zai fi mayar da hankali ne kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da maƙwabtanta, da kuma sauran sassa na duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo.

    Ku kasance da mu.