Abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 02/12/2025.

Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya 02/12/2025.

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida da Isiyaku Muhammad

  1. Birtaniya ta soki jinkirin shigar da tallafi zuwa Gaza

    ...

    Asalin hoton, EPA

    Gwamnatin Birtaniya ta yi suka kan jinkirin shigar da tallafin jin kai zuwa Gaza, bayan sama da tantuna 1,100 da ta tura sun ɗauki fiye da shekara guda kafin su isa.

    Sakatariyar harkokin waje, Yvette Cooper, ta ce duk da tsagaita wuta tsakanin Hamas da Isra’ila, har yanzu ana samun cikas wajen kai tallafin da Birtaniya ta biya, lamarin da ya ƙara taɓarɓarewar rayuwa a Gaza inda MDD ta ce mutane miliyan 1.5 na buƙatar mafaka cikin gaggawa kafin lokacin sanyi.

    Tantunan wanda kowanne zai iya daukar iyali guda sun isa Gaza a ranar Litinin, kuma ana sa ran ƙarin wasu su isa a wannan makon.

    Gwamnatin Birtaniya ta ce za su taimaka wa kimanin mutum 12,000 su samu mafaka a lokacin sanyi.

    Cooper ta ce "jinkirin kai tallafi ba kamata ya ci gaba da ɗorewa ba, inda ta buƙaci buɗe dukkan hanyoyin shiga Gaza domin ingantaccen tallafi ya riƙa isa ba tare da tangarɗa ba."

    Fiye da mutane miliyan 1.9 kimanin kashi 90 na al'ummar Gaza kenan sun rasa muhallansu tun bayan ɓarkewar rikicin Isra’ila da Hamas a 2023, in ji MDD.

    Cooper ta ce "shigowar tantunan wani muhimmin mataki ne, amma akwai bukatar karin tallafi da kuma gaggawar sake gina Gaza.

  2. An samu ƙarin mace-mace sakamakon ambaliyar ruwa a Indonesia

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Akwai rahotannin da ke cewa an samu rashe rashe da kuma raunuka a lardin Sumatra da ke arewacin indonesia a yayin da mutanen da suka tsira daga mummunar ambaliyar ruwa ke ƙoƙarin neman ɗauki.

    Har yanzu ba a fara kwashe mutane daga inda ambaliyar ta illata ba yayin da ake ganin yadda jami'an ceto ke fuskantar ƙalubale saboda ƙoƙarin kai wa ga wadanda ambaliyar ta rutsa da su.

    Har yanzu tallafin gwamnati bai kai ga wasu yankuna ba inda ake cewa an samu matsalar sace-sace da ɓalla shaguna.

    Tuni dai ƙungiyoyin agaji suka yi gargadin cewa akwai yiwuwar a ci gaba da samun wadanda za su rasa ransu ba wai saboda ambaliyar ba, sai don yunwar da ta addabesu da kuma rashin yi musu a rauni da suka ji. do ma short headline for this

  3. Assalamu Alaikum

    Barkanmu da sake saduwa a shafin labarai kai-tsaye na BBC Hausa a yau Talata.

    Shafin na yau zai fi mayar da hankali ne kan abubuwan da ke faruwa a Najeriya da maƙwabtanta, da kuma sauran sassan duniya.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kuma kallon bidiyo.

    Ku kasance da mu.