Yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya 03/03/2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku rahoto kan yaƙin Iran da Amurka da Isra'ila da kuma abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Talata 3 ga watan Maris 2026.

Taƙaitattu

  • Latsa nan domin shiga zaurenmu na Whattsapp
  • Ƴan shi'a sun yi zanga-zangar nuna goyon bayan Iran a Legas
  • Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta kai hari kan ofishin shugaban ƙasar Iran
  • Iran na ci gaba da luguden wuta kan Isra'ila da sansanonin sojin Amurka
  • Yawan sojojin Amurka da aka kashe a yaƙin Iran ya kai 6
  • An kai hari kan ofishin jakadancin Amurka a Saudiyya
  • Hezbollah ta ce ta kai hari kan sansanonin sojin Isra'ila uku
  • Farashin gas na ci gaba da tashi sakamakon rikicin Gabas ta Tsakiya
  • Mutum shida da za su iya maye gurbin Ayatollah Ali Khamenei

Rahoto kai-tsaye

Daga Aisha Babangida, Haruna Kakangi da Abdullahi Bello Diginza

  1. Iran na ci gaba da luguden wuta kan Isra'ila da sansanonin sojin Amurka

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Iran na ci gaba da yin luguden wuta kan Israila da sansanonin sojin Amurka a ƙasashen gabas ta tsakiya.

    Saudiyya ta ce wasu jirage marasa matuƙa biyu na Iran din sun kai hari kan Ofishin Jakadancin Amurka da ke babban birnin ƙasar, Riyadh.

    Ma’aikatar tsaron ƙasar ta ce ta samu nasarar kakkaɓo wasu jirage marasa matuƙa guda takwas da ke kan hanyarsu ta zuwa babban birnin, da kuma birnin Al-Kharj da ke kusa.

    Ofishin Jakadancin Amurka ya bai wa ‘yan ƙasarsa da ke zaune a masarautar shawarar su nemi mafaka a inda suke.

    Ƙasashen Qatar da Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa da kuma Isra’ila su ma sun bayar da rahoton cewa makamai masu linzami na ta yawo a sararin samaniyarsu.

    Yanzu haka Amurka ta bukaci yan kasarta da ke zaune a kasashe goma sha biyu na yankin su fice cikin gaggawa.

  2. Yawan sojojin Amurka da aka kashe a yaƙin Iran ya kai 6

    ...

    Asalin hoton, Getty Images

    Rundunar sojin Amurka ta tsakiya, wato Centcom ta ce adadin sojojin Amurka da suka mutu a yaƙin Iran ya kai shida.

    A cikin sanarwar da rundunar ta fitar, ta bayyana cewa sojojinta sun gano gawarwakin wasu sojoji biyu da a baya ba a san inda suke ba, daga wani gini da aka kai wa hari a farkon luguden wutar da Iran ta soma kai wa a yankin.

    Sanarwar ta kara da cewa yaƙi na ci gaba da gudana, duk da asarar da aka samu.

    Rundunar ba ta yi ƙarin bayani kan inda harin ya fi ƙamari ba ko kuma ko akwai ƙarin sojojin da suka jikkata.

    Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da rikici ke kara tsananta a yankin ƙasashen gabas ta tsakiya inda ake ci gaba da musayar wuta tsakanin Amurka da Isra'ila da Iran

  3. Mutum shida da za su iya maye gurbin Ayatollah Ali Khamenei

    ....

    Asalin hoton, BBC Monitoring

    Kamar yadda kundin tsarin mulkin Iran ya tanada, Majalisar Masana ta ƙasar – wadda ta ƙunshi manyan malaman addini 88 – ce za ta zaɓi mutumin da zai zamo sabon jagoran addinin ƙasar.

    Ana zaɓen wakilan majalisar malaman Iran ne a duk shekara takwas, kuma dole ne sai Majalisar Magabata ta ƙasar ta tantance su.

    Masu goyon bayan Ali Khamenei ne suka lashe dukkanin kujerun majalisar a zaben shekara ta 2024, inda daga baya aka samu giɓi a kujeru huɗu bayan mutuwar wakilansu – cikin har da Ebrahim Raisi, waɗanda za a cike gurbinsu a zaɓen cike gurbi da za a yi a watan Mayun 2026.

    Sashe na 111 na kundin tsarin mulkin ƙasar ya tanadi cewa a samar da wata majalisa ta mutum uku ta wucin-gadi, wadda za ta gudanar da al'amuran ƙasar kafin zaɓen sabon jagoran addini.

    Kwamitin riƙon-ƙarywar zai ƙunshi shugaban ƙasa Massoud Pezeshkian, da babban alƙalin alƙalan ƙasar Gholamhossein Mohseni Ejei da kuma malami masanin shari'a guda ɗaya daga Majalisar Magabata ta ƙasar.

  4. Assalamu alaikum

    Masu bin shafin BBC Hausa kai-tsaye barkanmu da safiyar wannan rana ta Talata.

    Kamar kullum, yau ma za mu kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya.

    Aisha Babangida da Abdullahi Bello Diginza ke fatan sake kasancewa da ku a daidai wannan lokaci.

    Za ku iya leƙawa shafukan sada zumuntanmu na intanet, da facebook da X da kuma whatsapp domin karanta sauran labarai da kallon bidiyo da tafka muhawara.