Mutum uku sun mutu, 30 sun maƙale bayan ruftawar mahaƙar ma'adinai a Ghana

Hukumomi a kudancin Ghana sun ci gaba da aikin ceton masu haƙar ma'adinai ba bisa ƙa'ida ba da ake fargabar sun makale a ƙarƙashin wata mahaƙa da ta rufta a ranar Laraba.
An tabbatar da mutuwar mutum uku, yayin da wani mutum guda ke kwance a asibitin cikin mawuyacin hali, bayan ruftawar mahaƙar da ke ƙauyen Akyem Wenchi a gundumar Denkyembour a yankin gabas.
Jami'ai sun ce ana fargabar akwai mutum 30 da suka maƙale bayan ruftawar mahaƙar.
Kawo yanzu ba a san dalilin da ya haifar da ruftawar mahaƙar ba.
Jami'an tsaro sun fice daga yankin, bayan da wasu fusatattun matasa da mazauna yankin suka mamaye mahaƙar a lokacin da ake aikin ceton.

Shugaban yankin, wanda kuma shi ne shugaban majalisar tsaron yankin, Umar Ahmed ya ce ''hayaniyar mutane ce ta hana tawagar ceton ci gaba da aikinsu''.
“Dole mu bar yankin, saboda ya zama babu tsaro ga ma'aikatan namu, musamman lokacin da fusatattun matasan suka isa yankin suna rera waƙoƙi.''
Umar Ahmed ya shaida wa kafofin yaɗa labaran ƙasar cewa ji yayi kamar yana cikin barazana, don haka ya fice daga yankin don kare kansa.
Ƴansanda a yankin Akwatia sun jima suna fama da masu haƙar ma'adinai ba bisa ƙa'ida ba a yankin.



