Kana amfani da shafin BBC mai bayyana rubutu kawai (babu hoto) domin rage cin data. Idan ana so a ga hotuna da bidiyo sai a koma babban shafinmu.

Koma shafi mai hoto

Samu ƙarin bayani kan shafin tattalin data

Labarin wasanni daga 08 zuwa 13 ga watan Fabrairu 2026

Wannan shafi ne da ke kawo muku muhimman abubuwan da ke faruwa a duniyar wasanni daga Lahadi 08 zuwa 13 ga Fabrairu 2026

Taƙaitattu

Rahoto kai-tsaye

Mohammed Abdu

  1. , Daga Jaridu

    Manchester City na shirin lale fam miliyan 100 domin ɗauko ɗanwasan tsakiya na Nottingham Forest da Ingila Elliot Anderson. (Teamtalk)

    Bayern Munich na sa ido kan ɗanwasan Atletico Madrid da Argentina Julian Alvarez, wanda Arsenal ke hari. (Christian Falk)

    AC Milan na fatan Fulham za ta saye ɗanwasanta na Najeriya mai shekara 26 Samuel Chukwueze, wanda ke taka leda a Ingila a matsayin aro. (Gazzetta - in Italian)

    Manchester United na son ɗanwasan tsakiya na Borussia Monchengladbach mai shekara 23 Rocco Reitz, wanda farashinsa ya kai fam miliyan 35. (Fichajes - in Spanish)

  2. Dyche ya ce baya fuskantar barazana a aikin kocin Forest, Nottingham Forest

    Kocin Nottingham Forest, Sean Dyche, ya yi watsi da raɗe-raɗin da ake yi kan aikinsa, inda ya jaddada cewa wasa guda ba zai iya tantance makomarsa ba a ƙungiyar.

    Forest za ta karɓi baƙuncin Wolverhampton ranar Laraba a gasar Premier League karawar mako na 26, ta kuma san akwai jan aiki a gabanta, saboda tana ta 17 - wato ta huɗun karshen teburi.

    An zabi Dyche a matakin fitatcen kociyan Premier a watan Janairu, bayan wasa hudu ba tare da rashin nasara ba, sai dai Leeds United ta doke Forest 3-1 a Elland Road ranar Juma'a.

    Kociyan ya yi watsi da batun da ake cewa rashin nasarar da ya yi a gidan Leeds ta jefa shakku kan makomarsa a Forest.

  3. Ko United za ta ci wasa na biyar a jere a Premier League?, Premier League

    Wasan West Ham United da Manchester United zai ja hankalin magoya baya da za a buga ranar Talata.

    West Ham tana ta 18 cikin ƴan ukun karshe, United kuwa tana ta huɗu a saman teburin babbar gasar tamaula ta Ingila.

    A wasan farko a Old Trafford a cikin watan Disamba tashi suka yi 1-1.

    Michel Carrick mai aikin rikon ƙwarya na fatan cin wasa na biyar a jere a Premier League. bayan doke Manchester City da Arsenal da Fulham da kuma Tottenham tun bayan maye gurbin Ruben Amorim.

  4. , Daga Jaridu

    Ana sa ran Cristiano Ronaldo zai kawo ƙarshen yajin aikin da yake yi a Al-Nassr inda zai ci gaba da taka leda a gasar Saudiyya ta Saudi Pro League a ranar Asabar. Ɗanwasan na Portugal mai shekara 41 ya ƙauracewa wasa biyu inda ya nuna fushinsa kan yadda ake tafiyar da ƙungiyar. (Sky Sports)

    Zaɓen shugabancin Barcelona ne zai tantance makomar ɗanwasan gaba na Ingila Marcus Rashford a Nou Camp. Makomar ɗanwasan na Manchester United ta dogara ne da sake zaɓen Joan Laporta a matsayin shugaban Barca. (Times - subscription required)

    Manchester United na harin ɗanwasan gaba na Everton da Senegal Iliman Ndiaye mai shekara 25 idan har Rashford ya zama mallakin Barcelona. (Caught Offside)

    Bournemouth na shirin danƙarawa matashin ɗanwasan gaba na Faransa Eli Junior Kroup kwantaragi mai gwaɓi yayin da manyan ƙungiyoyi irinsu Chelsea da Liverpool da Real Madrid da Paris St-Germain ke ribibinsa. (Sun)

  5. Tottenham tana bukatar maki uku a kan Newcastle, Premier League

    Mai horar da Tottenham, Thomas Frank ya ce suna matukar bukatar maki uku a kan Newcastle United ranar Talata a Premier League.

    Sai dai ya kara da cewar bai sani bo ko Dejan Kulusevski zai kara buga musu tamaula nan gaba a kakar nan.

    Tottenham mai fama da ƴan wasa da yawa da ke jinya tana ta 15 a kasan teburi.

    Wasa biyu ta ci daga karawa 16 a Premier League - a wasan farko a bana a cikin Disamba sun tashi 2-2 a St James Park da Newcastle.

  6. Kociyan Chelsea yana jin daɗi da ƴan wasansa ke sa ƙwazo, Chelsea

    Kocin Chelsea, Liam Rosenior, ya yaba wa ƴan wasansa kan jajircewar da suke da ta kai suke samun nasarori tun bayan da ya karɓi aiki a watan da ya gabata – wanda wasa biyu aka doke shi - shi ne a hannun Arsenal gida da waje a Carabao Cup.

    Chelsea wadda ke karɓar bakuncin Leeds United ranar Talata - tana ta biyar din teburi da tazarar maki daya tsakani da Manchester United ta huɗu a teburin Premier League.

    Wasan farko da ta kara da Leeds United a Elland Road a cikin Disambar bara, Leeds ce ta ci 3-1.

  7. Za a raba jadawalin Nations League ranar Alhamis, Nations League

    Ranar Alhamis za a raba jadawalin Nations League kakar bana a Brussels.

    Ingila tana League A, bayan da aka raba tawaga 16 zuwa tukwane huɗu kowanne kan kwazon kowacce kasa a fannin taka leda a Turai.

    Ingila tana tukunya ta uku - kenan za a iya haɗa ta da ko dai Sifaniya ko kuma Faransa, waɗanda suke tukunyar farko – kuma watakila ma a haɗa ta da Wales wadda ke tukunya ta hudu.

    Za a fara wasannin cikin rukuni a Satumba zuwa Oktoba da yin karawa biyu a cikin watan Nuwamba.

    A cikin watan Maris din baɗi ake sa ran buga zagayen kwata fainal, yayin da za a fafata a daf da karshe a cikin watan Yuni.

  8. Za a ci gaba da wasannin mako na 26 a Premier ranar Talata, Premier League

    Ranar Talata za a fara wasu daga wasannin mako na 26 a gasar Premier League da za a yi fafatawa huɗu.

    • Chelsea da Leeds United
    • Everton da Bournemouth
    • Tottenham da Newcastle
    • West Ham United da Manchester United
  9. Wannan ce kaka mafi wahala da na taɓa fuskanta a matakin koci - Slot, Liverpool

    Kocin Liverpool, Arne Slot, ya ce wannan kakar ita ce mafi wahala da ya taba fuskanta a matsayin mai horaswa, ya kuma bayyana cewa ƙungiya ba ta taka leda yadda ya dace da matsayinta.

    Rashin nasara da Liverpool ta yi a hannun Manchester City a Anfield ranar Lahadi, ya sa mai rike da kofin Premier League ta yi kasa zuwa mataki na shida a teburi da tazarar maki huɗu tsakani da Chelsea ta biyar.

    Liverpool na da maki 39 a teburin iri ɗaya da na Brentford da ke matsayi na bakwai.

    Slot ya maye gurbin Jurgen Klopp a watan Yunin 2024, kuma ya jagoranci ƙungiyar ta lashe Premier League a bara a kakarsa ta farko, kuma na 20 jimilla da Liverpool ta ɗauka a tarihi.

    Sai dai a wannan kakar sun fuskantar koma baya duk da kashe kusan fam miliyan 450 wajen sayen sabbin ƴan wasa kan fara kakar bana, ciki har da Alexander Isak wanda aka saya kan fam miliyan 125 — mafi tsada a tarihin Birtaniya.

    A kakar bana Liverpool ta yi nasara 11 da kunnen doki shida, sannan ta sha kashi a wasa takwas a babbar gasar tamaula ta Ingila.

  10. Watford ta naɗa Still sabon kociyanta, Watford

    Ƙungiyar Watford da ke buga Championship ta nada Edward Still a matsayin sabon babban kocinta, tuni ya sanya hannu kan kwantiragin kaka biyu da rabi.

    Still ya karɓi ragamar jagoranci ƙungiyar da ke Vicarage Road, bayan murabus da Javi Gracia ya yi, wanda ya shafe wata uku kacal a kan mukamin.

    Matashin kocin mai shekaru 35, ya yi mataimakin a kungiyar Anderlecht ta kasar Belgium.

  11. Hurzeler na rarrashin magoya bayan Brighton, Brighton

    Kocin Brighton da ke fuskantar barazara kora, Fabian Hurzeler, ya amince cewa yan wasa na fama da rashin kwarin gwiwa - yayin da yake ta kokari kwantar da hankalin magoya bayan kungiyar da suka nuna bacin ransu a karshen mako.

    An yi wa Brigton ihu, bayan shan kashi da ci 1-0 a ranar Lahadi a hannun abokiyar hamayya Crystal Palace a filin Amex Stadium, inda wasu magoya baya ke kira a kori Hurzeler daga aikin.

    Brighton na fuskantar kalubale, wadda ta ci wasa ɗaya daga 12 da ta buga a baya-bayan nan da hakan ya sa ta yi kasa zuwa mataki na 14 a teburin Premier League.

  12. Howe ya ce zai yi ritaya idan ya ji ba shi ne ya dace da kocin Newcastle ba, Newcastle United

    Babban kocin Newcastle United, Eddie Howe, ya ce zai iya ajiye aiki, idan ya ga cewa ba shi ne mutumin da ya dace da jagorantar kungiyar ba.

    Magoya bayan Newcastle sun yi wa ƴan wasa ihu bayan sun sha kashi 3-2 a hannun Brentford a filin St James' Park a ranar Asabar, hakan ya kara sa ƙungiyar ta ci karo da babban koma baya.

    Howe ya nuna bakin ciki matuka bayan ta shi wasan da aukar alhakin rashin nasarar, inda Newcastle ta koma ta 12 a teburin Premier League.

    Howe — wanda ya lashe Carabao Cup a bara da kawo karshen shekara kusan 70 rabon da kungiyar ta dauki kofi — ya jaddada cewa babu shakku a ransa shi ne mutumin da ya dace da aikin horar da Newcastle.

  13. , Gasar Olympic

    Masu shirya gasar Olympics a Milan–Cortina a 2026 sun ce suna bincike kan dalilin da ya sa lambobin yabo na Olympics ke karyewa, bayan ƴan wasa da dama sun yi korafi.

    ’Yan wasa biyu daga Amurka da suka lashe zinariya, Breezy Johnson da Alysa Liu, sun bayyana cewa igiyar ratayawa ta tsinke da lambar ta karye jim kaɗan bayan an mika musu kyautar.

  14. , Daga Jaridu

    Ɗanwasan tsakiya na Newcastle da Italiya Sandro Tonali, mai shekara 25, na kan gaba cikin waɗanda Manchester United ke farauta domin maye gurbin ɗanwasan tsakiya na Brazil Casemiro, mai shekara 33 a wannan bazara. (Telegraph - subscription required)

    Liverpool za ta ba ɗanwasan gaba na Italiya Federico Chiesa damar tafiya kuma tana son tsakanin fam miliyan 21.7 zuwa miliyan 26 yayin da Juventus da Napoli da Roma ke buƙatarsa. (Caughtoffside)

    Tottenham ba ta buƙatar mallakar ɗanwasan gaba na Faransa Randal Kolo Muani da ta karɓo aro daga Paris St-Germain. (Teamtalk)

    Liverpool na shirin sake ɗauko ɗanwasan Ingila Jarell Quansah daga Bayer Leverkusen a baɗi. (Football Insider)

    Alex Jimenez na shirin kammala yarjejeniyar shekara biyar zuwa Bournemouth daga AC Milan kan fam miliyan. (Fabrizio Romano)

    Manchester City na son ɗauko ɗanwasan tsakiya na Everton da Ingila Kiernan Dewsbury-Hall kan fam miliyan 40. (Fichajes - in Spanish)

  15. Laporta ya yi murabus domin sake neman shugabantar Barca, Barca

    Joan Laporta ya yi murabus daga mukamin shugaban Barcelona domin neman sake tsayawa takara, inda ake sa ran yin zaɓe ranar 15 ga watan Maris.

    Laporta, wanda ya hau karagar mulki a watan Maris a 2021 bayan ya samu ƙuri'u kaso 54 cikin 100, ya sauka daga mukamin bayan kusan shekaru biyar yana jagoranci, bisa tanadin dokokin ƙungiyar.

    Mataimakin shugaba, Rafa Yuste ne zai rike mukamin a matakin rikon kwarya har zuwa gudanar da zaben wanda zai ja ragamar Barcelona nan gaba.

    Kimanin mambobin Barcelona 100,000 da suka kai shekarun da doka ta tanada kuma suka yi akalla shekara guda suna mambobi ne ke da damar kada kuri’ar.

  16. Ko Manchester City za ta ci gaba da kalubalantar Arsenal?, Manchester City

    Ƙungiyar da Pep Guardiola ke jan ragama, za ta koma Etihad ta buga wasa biyu a Premier League da Fulham da kuma Newcastle United.

    Sai dai bayan wasan Fulham za ta karɓi bakuncin Salford mai buga League Two a zagaye na huɗu a FA Cup

    Haka kuma City tana da damar rage tazarar maki ya koma uku tsakani da Arsenal, sakamakon da za ta fuskanci Fulham ranar Laraba, ita kuwa Gunners sai a ranar Alhamis za ta je Brentford.

    City za ta buga wasan karshe a watan Fabrairu a Premier da zuwa gidan Leeds United, sannan ta fara fafatawa a watan Maris da fuskantar Nottingham Forest a Etihad.

  17. Yadda ƴan shida suke a teburin Premier League, Premier League

    Ga yadda sakamakon wasannin Lahadi ya shafi matsayin ƴan shida a kan teburin Premier League bayan kammala mako na 25..

    Arsenal ta kara sa kokarin tun bayan rashin nasara a gida a hannun Manchester United a watan jiya, inda ta ci wasa huɗu tun daga lokacin har da doke Sunderland a Emirates.

    Manchester City ma ta sa ƙwazo tun bayan da Manchester United ta doke ta 2-0 a Old Trafford a hannun kociyan riƙon ƙwarya, Micheal Carrick.

    Sai dai ƙungiyar Etihad ta tashi 2-2 a gidan Tottenham, amma ta je ta ci Liverpool 2-1 ranar Lahadi a Anfield.

    Da wannan sakamakon City, wadda take ta biyun teburi da tazarar maki shida tsakani da Arsenal ta ɗaya - tana da tazarar maki uku tsakani da Aston Villa ta uku.

    Manchester United ta huɗu da tazarar maki uku tsakani da Aston Villa ta uku.

    Chelsea ce ta biyar ɗin teburi da tazarar maki ɗaya tsakani da United da kuma Liverpool ta shida mai tazarar maki biyar tsakani da Chelsea ta biyar a teburin Premier League a rige-rigen neman gurbin Champions League a baɗi.

  18. , Daga Jaridu

    Inter Milan za ta bai wa kocinta Cristian Chivu damar tsawaita kwantiraginsa da shekara guda, wanda zai ci gaba har zuwa 2028, da kuma karin albashi a karshen kakar wasa. (Corriere dello Sport)

    Dole ne dan wasan gaba na Argentina Paulo Dybala, mai shekaru 32, da kuma dan wasan tsakiya na Italiya Lorenzo Pellegrini, mai shekaru 29 su rage albashinsu idan suna son ci gaba da zama a Roma, yayin da kwantiragin 'yan wasan biyu zai kare a lokacin bazara. (Gazzetta dello Sport)

    Dan wasan tsakiya na Italiya Sandro Tonali, mai shekaru 25, zai iya neman barin Newcastle idan Magpies ta kasa tsallakawa zuwa gasar zakarun Turai a kakar wasa mai zuwa. (Football Insider)

    Sai dai ita ma Newcastle din na neman ɗan wasan tsakiya na Lyon mai shekaru 23 Tyler Morton a matsayin wanda zai iya maye gurbin Tonali, yayin da Crystal Palace da Nottingham Forest suma ke sha'awar tsohon ɗan wasan na Liverpool (Caughtoffside)

  19. City ta rage tazarar maki tsakaninta da Arsenal a Premier League, Premier League

    Liverpool ta yi rashin nasara 2-1 a Anfield a wasan mako na 25 da suka buga ranar Lahadi a Anfield.

    Liverpool ce ta fara cin ƙwallo ta hannun Szoboszlai a zagaye na biyu, bayan da minti 45 na farko ba ci a tsakaninsu.

    City ta farke ta hannun Bernardo Silva daga baya Erling Haaland ya kara na biyu a bugun fenariti daf a tashi.

    Liverpool ta karasa karawar da ƴan wasa 10 a cikin fili, bayan da aka bai wa Szoboszlai jan kati, sakamakon da ya rike rigar Haaland a lokacin da ƙwallo zai shiga ragar ƙungiyar Anfield.

    Da wannan sakamakon City ta ci gaba da zama ta biyu da maki 50 da tazarar shida tsakani da Arsenal, wadda ta doke Sunderland ranar Asabar.

    Kenan City ta doke Liverpool gida da waje a bana, bayan nasara 3-0 a cikin watan Nuwambar 2025 a Etihad, karon farko tun bayan 1936/37.

    Wannan shi ne karo na biyu da City ta doke Liverpool a Anfield a fafatawa 23, bayan da Liverpool ta yi nasara 14 da canjaras bakwai.

    Rabonda City ta doke Liverpool a gida tun 4-1 a cikin watan Fabrairun 2021.

  20. Kano Pillars ta samu maki uku a kan Remo Stars, Premier League ta Najeriya

    Kano Pillars ta yi nasarar cin Remo Stars 1-0 a wasan mako na 25 a Premier League da suka buga ranar Lahadi.

    Pillars ta ci ƙwallon ta hannun Lius Dadong a zagaye na biyu a karawar da suka yi a filin wasa na Sani Abacha da ke Kofar Mat a jihar Kano, Najeriya.

    Da wannan sakamakon ƙungiyar da ake kira sai masu gida ta yi sama zuwa mataki na 14 a teburi da maki 31, ita kuwa Remo Stars ta nutsa kasan teburi ta 19 da maki 26.

    Ga sakamakon wasannin da aka buga ranar Lahadi:

    • Abia Warriors 0-0 Enugu Rangers International
    • Ikorodu City 2-0 Niger Tornadoes
    • Kano Pillars 1-0 Remo Stars
    • Kun Khalifat 2-0 Shooting Stars
    • Nasarawa United 1-1 Bayelsa United
    • Plateau United 1-0 Kwara United
    • Warri Wolves 0-0 El Kanemi Warriors
    • Wikki Tourists 3-3 Katsina United

    An ci karo da cikas a wasan Wikki da Katsina da yamutsi

    Tun a ranar Asabar Bendel Insurance ta ci Enyimba 2-0.